Zazzaɓin Lassa ya kashe mutum 151 a Nijeriya bana — NCDC
Published: 22nd, July 2025 GMT
Hukumar yaƙi da cututtuka masu yaɗuwa a Nijeriya (NCDC) ta ce adadin mutanen da zazzaɓin lassa ya kashe bana sun kai 151 a fadin kasar.
Cikin wata sanarwa da NCDC ta wallafa a shafinta na X ranar Litinin, ta ce yawan kisan da cutar zazzaɓin lassa ke yi ya ƙaru daga kashi 17.3 cikin 100 da aka samu a bara.
Sanarwar ta ce an yi bitar alkaluman mamatan a bana ne bisa la’akari adadin waɗanda suka kamu kuma ta yi ajalinsu a shekarar 2024.
Hukumumar ta ce alkaluman mamatan ya kai kashi 18.9 cikin 100 na waɗanda suka kamu da ita a wannan shekara.
Sanarwar ta ce kwanan na an samu ƙarin mutum 11 da suka kamu da cutar a cikin jihohin ƙasar shida, lamarin da ya mayar da jimullar waɗanda aka tabbatar sun kamu da cutar a wannan shekarar mutum 800.
Kazalika, sanarwar ta ce kashi 90 cikin 100 na waɗanda suka kamu da cutar suna cikin jihohin Ondo da Bauchi da Edo da Taraba da kuma Ebonyi ne.
Cutar zazzaɓin lassa dai tana yaɗuwa ne ta hanyar kashin ɓera, kuma cuta ce da ke iya yaɗuwa daga mutum zuwa mutum.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: zazzaɓin Lassa
এছাড়াও পড়ুন:
Kungiyar Hamas Ta Yi Suka Kan Kame ‘Yan Gwagwarmaya Da Hukumar Falasdinawa Ke Yi
Jami’in kungiyar Hamas ya bayyana cewa: Kamen da hukumar Falasdinawa ta yi wa ‘yan gwagwarmaya a yankin Gabar Yammacin Kogin Jordan yana nuna goyon baya ne ga ‘yan mamayar Isrta’ila
Jami’in kungiyar Hamas Abdel Rahman Shadid ya bayyana cewa: Kamen da jami’an tsaron Hukumar Falasdinawa suka yi na wani gungun ‘yan gwagwarmaya a Nablus da Jenin, da kwace makamansu, da kuma ci gaba da fatattakar ‘yan gwagwarmaya a duk fadin yankin gabar yammacin kogin Jordan, yana nuni da ci gaba da goyon bayan gwamnatin mamayar Isra’ila ce da murkushe al’ummar Falastinu.
A cewar cibiyar yada labaran Falasdinu, Shadid ya jaddada a cikin wata sanarwa da ya fitar cewa: Kamen da jami’an tsaron hukumar cin gashin kan Falasdinawa suka yi kan ‘yan gwagwarmaya da kuma fitattun al’umma da masanan Falasdinawa, biyan ladar moro-maron yahudawan sahayoniyya ne da jami’an hukumar Falasdinu suka ci.
Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da ake ruguza gidajen mutane a Jenin, tare da koran dubban mutane a Tulkarm, ana kuma kwace yankunan mutane a gabar yammacin kogin Jordan.
Shadid ya bayyana cewa: Wadannan ayyuka suna nuna manufar Hukumar Cin gashin Falasdinawa ne na ganin ta raba ‘yan gwagwarmaya da yankin gabas yammacin kogin Jordan, tare da barin Falasdinu a bude ga sojojin mamayar Isra’ila gungun ‘yan ta’addan su aiwatar da tsare-tsaren Sanya Falasdinawa gudun hijira.