Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya bayyana cewa kofar tattaunawa da Amurka kan shirinta na makamashin Nukliya a bude take, amma kafin haka sai gwamnatin kasar Amurka ta biya diyyar kura kuran da ta yi a bayan.

A wata hirar da yayi da Jaridar Le Monde na kasar Faransa Aragchi ya kara da cewa da farko Amurka yakamata ta canza halayenta, na rashin kaiwa kasar Iran hare-hare a lokacin tattaunawa.

Ya ce diblomasiyya hanyace mai tituna biyu na zuwa da komawa, amma Trump ya zo ya rufe dayar.  Kuma tattaunawar diblomasiyya a wajen Iran a ko yauce a bude yake, Hare-haren da jiragen yakin Amurka suka kai kan kasar Iran a cikin yakin kwanaki 12 keta hurumin diblomasiyya ne, kuma dole Amurka ta biya diyyan Barnan da ta yi. Kuma wannan hakkin Iran ta nemi wannan hakkin.

Hakama kaiwa cibiyan makamashin Nukliya wanda ke karkashin kula na hukumar IAEA kuskure ne. don babu tabbaci daga hukumar kan cewa shirin ya karkata daga na zaman lafiya. Wannan ma sai Amurka ta biyya diyyar yin haka.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Aref Ya Bayyana Cewa: Iran Ba Ta San Kalmar Mika Wuya Ba A Al’adunta Da Tsaronta

Mataimakin shugaban kasar na farko ya jaddada cewa: Kalmar “mika kai” ba ta da gurbi a al’adun siyasa da tsaron Iran

Mataimakin shugaban kasar Iran na farko Mohammad Reza Aref ya jaddada cewa: kalmar mika wuya ba ta da gurbi a al’adun siyasa da tsaron kasar.

Arif ya ce: Kamar yadda kuke gani kalmar “mika kai” ba ta da gurbi a al’adun siyasa da tsaron Jamhuriyar Musulunci ta Iran, yana mai jaddada cewa, su mutane ne masu wayewa, tare da ingantaccen tarihin al’adu wanda ya wuce dubban shekaru. Ba su neman yaki, kuma ba su fara shi ba. Sun yi imani da zaman lafiya da kwanciyar hankali, kuma a shirye suke don tattaunawa, amma ba za su mika wuya a kowane hali ba.

A wata hira da ya yi da KHAMENEI.IR, Aref ya jaddada cewa: An sha ambaton hakan, sannan kuma Jagoran juyin juya halin Musulunci ya bayyana cewa ba za mu fara yaki ba, amma idan aka tsokani Iran, to Iran zata mayar da martani, kuma haka yake har yanzu. Maƙiya ‘yan sahayoniyya ba za a taba amince da su ba. An dai tsagaita bude wuta a kasar Labanon, amma kamar yadda ake gani bayan tsagaita wuta an samun adadin shahidai masu yawa. Sadaukarwarsu ta kasance domin kare Iran ce.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Aref Ya Bayyana Cewa: Iran Ba Ta San Kalmar Mika Wuya Ba A Al’adunta Da Tsaronta
  •  Masu Kare Hakkin Dan’adam Suna Allawadai Da Takunkumin Amurka  Akann Jami’ar MDD A Falasdinu
  • Aragchi Ya Tattauna Da Bin Salman Kan Karfafa Zumunci Tsakanin Kasashen Biyu
  • UNHRC Ta Zartas Da Kudurin Sin Kan Kiyaye Hakkin Dan Adam Ta Hanyar Samun Ci Gaba
  • Iran Ta Musanta Neman Ci Gaba Da Gudanar Da Tattaunawa Da Amurka Kan Shirinta Na Makamashin Nukiliya
  • Aragchi: Amurka Tana Iya Farfado Da Tattaunawa Kan Shirin Makamashin Nukliyar Kasar Idan Tanaso
  • Aragchi: Amurka Tana Iya Farfado Da Tattaunawa Kan Shirin Makamashin Nukliya Kasar Idan Tanaso
  • Iran Za Ta Yi Nazarin Sabuwar Gayyatar Da Amurka Ta Yi Mata Na  Sabuwar Tattaunawa
  • Shugaban Kasar Iran Ya Ce; An Rusa Hanyar Tattaunawa da Iran Kan Shirin Na Makamashin Nukiliya Na Zaman Lafiya