Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umar Radda, tare da wasu mutane goma sha biyu na samun kulawa a asibiti bayan tsira daga wani hadarin mota da ya faru a kan hanyar Katsina zuwa Daura, a Jihar Katsina.

Hatsarin ya faru ne sakamakon taho-mu-gama da wata motar haya kirar Volkswagen a kusa da Tashar Motoci ta KTSTA da ke Daura.

Duk da cewa hukumar kiyaye hadurra ta kasa (FRSC) ba ta fitar da sanarwar hukumance dangane da lamarin ba, shaidu da hotunan da aka dauka daga wurin sun tabbatar da cewa motocin biyu sun lalace matuka.

Shaidun gani da ido sun shaida wa Radio Nigeria cewa motar gwamnan ba ta cikin sahun motocin rakiyar gwamnati a lokacin da hadarin ya faru.

Daya daga cikin wadanda suka taimaka wajen daukar wadanda suka jikkata zuwa Asibitin Tarayya na Daura, ya shaida wa Radiyon Najeriya cewa dukkan fasinjoji tara da ke cikin motar hayar sun samu raunuka.

“Mun kai su Asibitin Gwamnati na Daura inda ake kula da su yanzu,” in ji shi.

A halin yanzu, Kwamishinan Yada Labarai na Jihar Katsina, Alhaji Bala Salisu Zango, ya ziyarci fasinjojin motar hayar da suka jikkata a Asibitin Gwamnati na Daura, inda ya bayyana cewa gwamnatin jihar za ta dauki nauyin dukkan kudin maganinsu.

Bakwai daga cikinsu sun samu raunuka kadan ne kawai, yayin da biyu kuma suka sami karaya.

“Gwamnatin Jihar Katsina za ta biya dukkan kudin maganinsu kuma za ta ci gaba da kula da lafiyarsu har sai sun warke.” in ji Zango.

Ya kara da cewa gwamnan ma yana cikin koshin lafiya, kuma tuni aka sallame shi daga Asibitin Tarayya na Daura.

“Na yi magana da shi ta waya ba da dadewa ba, yana cikin koshin lafiya. An kwantar da shi tare da sauran wadanda suka jikkata a Asibitin Tarayya na Daura, kuma an sallame shi bayan an tabbatar da cewa lafiyarsa ta daidaita.”

Haka kuma, wata sanarwa da Sakataren Watsa Labarai na Gwamna Radda, Malam Kaula Mohammed ya sanya wa hannu ta tabbatar da cewa gwamnan yana cikin koshin lafiya.

A wani faifan bidiyo da aka wallafa a kafafen sada zumunta, gwamnan ya bayyana cewa shi da sauran wadanda hatsarin ya rutsa da su suna cigaba da samun kulawa.

 

Daga Isma’il Adamu.

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Gwamna Hadarin Mota Jihar Katsina

এছাড়াও পড়ুন:

Kamfanin Amazon na shirin sallamar ma’aikata 600,000 don maye gurbinsu da mutum-mutumi

Kamfanin Amazon, wanda shi ne na biyu a yawan ma’aikata a Amurka, zai sallami ma’aikata kusan 600,000 ta hanyar maye gurbin su da mutum-mutumi nan shekaru 10 masu zuwa.

Wani rahoton takardun cikin gida na kamfanin ne ta bayyana hakan, kamar yadda jaridar The New York Times ta Amurka ta wallafa.

Gwamnan Bauchi na neman ƙirƙirar sabbin ƙananan hukumomi 29 Majalisa ta amince Tinubu ya karɓo rancen dala biliyan 2.35

A cewar rahoton, wannan dabarar na fitowa ne daga masu lura da ma’aikata na kamfanin da alkaluman su ke nuna cewa kamfanin na iya kauce wa ɗaukar fiye da mutum 160,000 da ake bukata a Amurka nan da shekarar 2027.

Kamfanin dillancin kaya na Amazon ya taɓa bayyana cewa amfani da mutum-mutumi zai ba shi damar faɗaɗa kasuwancinsa zuwa ninki biyu na yawan kayayyakin da yake siyarwa nan da shekarar 2033, ba tare da ƙara yawan ma’aikata a Amurka ba.

Tarin takardun da aka tattara tare da hirarraki da jaridar ta gudanar ya nuna cewa wannan sauyi zai sa kamfanin ya zama ba ya buƙatar ɗaukar fiye da mutum 600,000 a cikin shekaru goma masu zuwa.

Sai dai Amazon ya ƙi amincewa da sakamakon binciken na jaridar.

A cikin wata wasika da ta aike wa The Independent, Amazon ya ce adadin mutum 600,000 ya fito ne daga wata takarda daga sashe guda na kamfanin, wanda ba shi da alaka da ɗaukar ma’aikata.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Namadi Ya Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3
  • Jerin Gwarazan Taurarinmu
  • Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace
  • Ranar Foliyo Ta Duniya: Muna Fatan Ganin Karshen Cutar Foliyo A Jihar Katsina -Zulaihat Dikko Radda
  • Sin Da Amurka Suna Taimaka Wa Juna Da Samun Wadata Tare
  • Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP
  • An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Kirkire-kirkire Da Bude Kofa Da Raba Damar Samun Ci Gaba A Colombo
  • Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma 
  • Kamfanin Amazon na shirin sallamar ma’aikata 600,000 don maye gurbinsu da mutum-mutumi