Gwamna Radda Da Makarrabansa Na Samun Kulawa A Asibiti Bayan Hatsarin Mota A Hanyar Daura
Published: 22nd, July 2025 GMT
Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umar Radda, tare da wasu mutane goma sha biyu na samun kulawa a asibiti bayan tsira daga wani hadarin mota da ya faru a kan hanyar Katsina zuwa Daura, a Jihar Katsina.
Hatsarin ya faru ne sakamakon taho-mu-gama da wata motar haya kirar Volkswagen a kusa da Tashar Motoci ta KTSTA da ke Daura.
Duk da cewa hukumar kiyaye hadurra ta kasa (FRSC) ba ta fitar da sanarwar hukumance dangane da lamarin ba, shaidu da hotunan da aka dauka daga wurin sun tabbatar da cewa motocin biyu sun lalace matuka.
Shaidun gani da ido sun shaida wa Radio Nigeria cewa motar gwamnan ba ta cikin sahun motocin rakiyar gwamnati a lokacin da hadarin ya faru.
Daya daga cikin wadanda suka taimaka wajen daukar wadanda suka jikkata zuwa Asibitin Tarayya na Daura, ya shaida wa Radiyon Najeriya cewa dukkan fasinjoji tara da ke cikin motar hayar sun samu raunuka.
“Mun kai su Asibitin Gwamnati na Daura inda ake kula da su yanzu,” in ji shi.
A halin yanzu, Kwamishinan Yada Labarai na Jihar Katsina, Alhaji Bala Salisu Zango, ya ziyarci fasinjojin motar hayar da suka jikkata a Asibitin Gwamnati na Daura, inda ya bayyana cewa gwamnatin jihar za ta dauki nauyin dukkan kudin maganinsu.
Bakwai daga cikinsu sun samu raunuka kadan ne kawai, yayin da biyu kuma suka sami karaya.
“Gwamnatin Jihar Katsina za ta biya dukkan kudin maganinsu kuma za ta ci gaba da kula da lafiyarsu har sai sun warke.” in ji Zango.
Ya kara da cewa gwamnan ma yana cikin koshin lafiya, kuma tuni aka sallame shi daga Asibitin Tarayya na Daura.
“Na yi magana da shi ta waya ba da dadewa ba, yana cikin koshin lafiya. An kwantar da shi tare da sauran wadanda suka jikkata a Asibitin Tarayya na Daura, kuma an sallame shi bayan an tabbatar da cewa lafiyarsa ta daidaita.”
Haka kuma, wata sanarwa da Sakataren Watsa Labarai na Gwamna Radda, Malam Kaula Mohammed ya sanya wa hannu ta tabbatar da cewa gwamnan yana cikin koshin lafiya.
A wani faifan bidiyo da aka wallafa a kafafen sada zumunta, gwamnan ya bayyana cewa shi da sauran wadanda hatsarin ya rutsa da su suna cigaba da samun kulawa.
Daga Isma’il Adamu.
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Gwamna Hadarin Mota Jihar Katsina
এছাড়াও পড়ুন:
NECO ta saki sakamakon jarabawar 2025
Hukumar Shirya Jarabawa ta Ƙasa (NECO), ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare (SSCE) na shekarar 2025.
Daga cikin ɗaliban da suka zana jarabawar guda 818,492, kashi 60.26 sun ci aƙalla darusa biyar da suka haɗa da Lissafi da Turanci.
Saudiyya ta saki ’yan Najeriya 3 da ta kama kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi Gwamnati ta fara duba yara marasa galihu kyauta a asibitin Aminu KanoShugaban NECO, Farfesa Dantani Ibrahim Wushishi, ya ce ɗalibai 1,367,210 suka yi rajistar jarabawar; maza 685,514 da kuma mata 681,696.
Amma daga cikinsu, ɗalibai 1,358,339 ne suka zana jarabawar.
Ya ce ɗalibai 1,144,496, wanda ya kai adadin kashi 84.26, sun samu darusa biyar ba tare da cin Lissafi da Turanci ba.
Sai dai an dakatar da sakin sakamakon makarantu takwas a Ƙaramar Hukumar Lamorde ta Jihar Adamawa saboda rikicin ƙabilanci da ya auku tsakanin 7 zuwa 25 ga watan Yuli, 2025.
Rikicin ya yi sanadin wanda ya hana zana jarabawar darusa 13 da takardu 29.
Hukumar na tattaunawa da gwamnati don sake bai wa ɗaliban damar rubuta jarabawar.
NECO ta kuma bayyana cewa an samu makarantu 38 daga jihohi 13 ds laifin aikatar satar amsa yayin zana jarabawa.
Za a gayyace su zuwa babban ofishin NECO kafin ɗaukar mataki a kansu.
Haka kuma, hukumar ta dakatar da mutum tara da ke aikin sanya ido sake kula da jarabawa saboda gazawarsu wajen hana satar amsa.
Mutanen da aka dakatar, uku sun fito daga Jihar Ribas, uku daga Babban Birnin Tarayya, da kuma mutum ɗai-ɗai daga Jihohin Neja, Kano da Osun.