Aminiya:
2025-07-23@05:09:06 GMT

Hisbah Ta Lalata Barasa Ta Naira Miliyan 5.8 A Jigawa

Published: 22nd, July 2025 GMT

Hukumar Hisbah ta ce ta kama tare da lalata barasa da ta kai kimanin naira miliyan 5.8 a karamar hukumar Kazaure ta Jihar Jigawa.

Kwamandan Hisbah a jihar Malam Ibrahim Dahiru ne ya bayyana haka a wata hira da manema labarai a Dutse, babban birnin jihar.

Jami’an tsaro sun dakile yunkurin Sanata Natasha na shiga harabar Majalisa Kamfanonin lantarki za su katse wuta kan bashin N5.

2trn da suke bin gwamnati 

Ya ce an gudanar da aikin ne karkashin jagorancin shugaban hukumar da ke Kazaure, Mansur Dabuwa, inda aka lalata katan 400 na barasa da darajar kudinsu ya kai naira miliyan 5.8.

Ya bayyana cewa an kama barasa da aka kona a lokacin samamen da aka kai a sassa daban-daban a yankin.

Kwamandan wanda ya jaddada cewa an haramta shan barasa a duk sassan jihar, ya kuma kara da cewa hukumar za ta ci gaba da yaki da munanan dabi’u da suka hada da shan barasa.

Don haka hukumar ta Hisbah ta bukaci mazauna yankin da su ci gaba da bai wa hukumar goyon baya da muhimman bayanai domin ta samu damar gudanar da ayyukanta yadda ya kamata.

Ya kuma shawarci mazauna garin da su daina aikata miyagun ayyuka da za su iya lalata tarbiyyar al’umma.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: barasa Jihar Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

Kamfanonin lantarki za su katse wuta kan bashin N5.2trn da suke bin gwamnati 

Kamfanonin wutar lantarki sun yi barazanar katse wutar a fadin Najeriya saboda tarin bashin da ya haura Naira tiriliyan 5.2 da suke bin gwamnati.

Taurin bashin, wanda ke barazana ga ci gaba da ayyukan kamfanoni, ya hada da Naira tiriliyan 1.2 na wutar da aka samar a watanni shidan farkon shekarar 2025, da Naira tiriliyan 2 daga 2024, da kuma bashin da aka gada tun daga 2015 wanda ya kai Naira tiriliyan 1.9.

Shugabar ƙungiyar kamfanonin samar da wutar lantarki, Dakta Joy Ogaji, ta bayyana cewa kamfanonin sun daɗe suna nuna kishin ƙasa ta hanyar ci gaba da samar da wuta duk da rashin biyan su kuɗaɗensu, amma yanzu sun gaji.

Ta bayyana cewa kudin da ake kashewa wajen samar da wuta a kowane wata yana kaiwa Naira biliyan 250, amma Gwamnatin Tarayya ta ware Naira biliyan 900 kacal a kasafin kuɗin 2025, kuma har zuwa yau ba a samu cikakken tabbacin samun wannan kuɗin ba.

An rufe masana’antu 1,724 bisa rashin bin dokokin aiki a Guinea NAJERIYA A YAU: Yadda tsadar taki ke hana noman masara da shinkafa

Ministan Makamashi, Adebayo Adelabu, ya bayyana cewa gwamnati tana ƙoƙarin rage wani ɓangare na bashin, amma har yanzu ba a bayyana yadda hakan zai faru ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Namadi Ya Sanya Hannu Kan Dokar Kafa Hukumar Hisba Ta Jihar Jigawa
  • Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ta Kai Ziyarar Gani Da Ido Kirikasamma
  • Kotu Ta Umarci Gwamnatin Bauchi Ta Biya Tsohon Akanta-Janar Naira Miliyan 100
  • Kamfanonin lantarki za su katse wuta kan bashin N5.2trn da suke bin gwamnati 
  • Tsohon Sakataren Gwamnatin Bauchi, Ibrahim Kashim, Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP
  • Gwamna Namadi Ya Jinjinawa Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Bisa Ayyukan Raya Kasa
  • Magudnar Ruwa Ta Yi Ajalin Rayuka Hudu A Zangon Kaya, Kano
  • Hukumar Kashe Gobara Ta Jihar Kwara Ta Taimaka Wajen Hana Lalacewar Wani Bene A Ilorin
  • Mataimakiyar Shugaban Majalisar Dinkin Duniya Ta Jinjinawa Gwamnan Kano Bisa Ayyukan Cigaban Jihar