UNICEF Ya Bukaci Jihar Kano Ta Bai Wa Yara Muhimmanci A Kasafin Kudi
Published: 23rd, July 2025 GMT
Asusun Kula da Yara na Majalisar Ɗinkin Duniya (UNICEF) ya nuna damuwa kan halin da yara ke ciki a jihar Kano, yana mai kira ga gwamnatin jihar da ta ƙara zuba jari a fannin lafiya, ilimi, da abinci mai gina jiki ta hanyar kasafin kuɗi da ya danganci makomar yara.
Shugaban ofishin UNICEF na Kano, Mista Rahma Rihood Muhammad Farah, ya bayyana hakan yayin wani taron tattaunawa da ‘yan jarida kan kasafin kuɗi mai la’akari da bukatun yara, inda ya gabatar da wasu alkalumma masu tayar da hankali dangane da rayuwar yara a jihar.
Farah ya ce jihar Kano na da yara fiye da miliyan 6 da rabi da ke ƙasa da shekaru 18, wadanda da dama daga cikinsu na fuskantar matsaloli masu tsanani kamar mace-macen yara, ƙarancin abinci mai gina jiki, da kuma rashin samun ingantaccen ilimi da kiwon lafiya.
Ya bayyana cewa, bisa ga rahoton MICS na 2021, yara 143,000 na mutuwa kafin su kai shekara biyar, yayin da kusan yara miliyan 2 da 900,000 ba su da cikakken rigakafi, sannan fiye da yara miliyan 4 na rayuwa cikin talauci.
Haka kuma, sama da yara miliyan 2 300,000 da suka kai shekarun makaranta suna zaune a gida ba tare da samun ilimi ba, wani hali da ya ce ya zama wajibi a sauya shi ta hanyar karfafa kasafin kuɗi na kula da yara.
Ya ce duk da wasu sauye-sauye da ake yi, fannin walwalar al’umma a Kano har yanzu na samun ƙarancin kudi, inda ya zargi sauyin kasafi da rashin daidaito a fannonin lafiya, ilimi da kare hakkin yara da janyo cikas ga cigaba.
Farah ya bayyana kasafin kuɗi mai kula da yara a matsayin wata dabara mai mahimmanci, fiye da ware kuɗi kawai ga makarantu da asibitoci.
A nasa jawabin, Mataimakin Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Kano, Hon. Muhammad Bello Butu Butu, ya tabbatar da kudurin majalisar na tabbatar da cikakken aiwatar da kasafin kuɗi ga ma’aikatu da hukumomi.
Sai dai ya soki wasu shugabannin ma’aikatu da hukumomi da rashin kokarin karɓar kuɗaɗen da aka ware musu da kuma gazawar aiwatar da su, duk da kokarin bangaren zartarwa wajen sakin kudin. Ya bayyana cewa kimanin kashi 35% na kasafin kuɗin jihar na zuwa fannin lafiya ne da ilimi.
Masu ruwa da tsaki da suka halarci taron, ciki har da ‘yan jarida, kungiyoyin farar hula, da ma’aikatun gwamnati, sun yi kira ga gwamnatin Kano da ta tabbatar da kasafin kuɗi mai la’akari da yara, ta ƙara yawan kuɗaɗen da ake warewa shirye-shiryen kula da yara, tare da tabbatar da gaskiya da rikon amana a wajen aiwatar da kasafin.
Daga Khadijah Aliyu
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: tabbatar da
এছাড়াও পড়ুন:
An sake kama shi a cikin ’yan fashi kwana 5 da fitowa daga kurkuku
’Yan sanda a jihar Legas sun kama wani tsohon fursuna tare da wasu mutum biyu bisa zargin hannu a jerin laifukan fashi da yankan aljihu a jihar kwana biyar da fitowa daga kurkuku.
Tsohon fursunan mai shekaru 25 da haihuwa, Segun Kolawole, an kama shi ne bayan kwana biyar da aka sako shi daga cibiyar gyaran hali ta Kirikiri, a jihar Legas.
Ana zargin ɗa da kashe mahaifinsa a Kano saboda hana shi ƙara aure Juventus ta ɗauki tsohon kociyan Italiya, Luciano SpalletiSauran wadanda aka kama tare da shi sun haɗa da Sodiq Isa mai shekaru 27 da Adekanmbi Ganiu mai shekaru 21.
Rahotanni sun nuna cewa an kama waɗanda ake zargin ne bisa laifukan yankan aljihun mutane da sauran laifukan sata a sassa daban-daban na jihar.
Mai magana da yawun ’yan sandan jihar, SP Abimbola Adebisi, ta tabbatar da cafke Kolawole, inda ta ce an kama shi da misalin ƙarfe 8 na safiyar Talata a kasuwar Oshodi, bayan jami’ai sun lura da motsinsa da ya zama abin zargi.
Adebisi ta ce an same shi da tsabar kuɗi ₦80,000 da wayar Infinix Note 40 Pro, waɗanda aka gano daga wani fashi da ya aikata a Opebi, inda ake zargin ya saci ₦200,000 da wayar daga hannun wani ɗan kasuwa da ke barci.
“Bincike ya ƙara tabbatar da cewa ya riga ya sayi sabbin kaya da takalma da wani ɓangare na kuɗin da ya sata, waɗanda suma aka kwato su daga hannunsa,” in ji ta.
Haka kuma, a wani samame daban da aka gudanar da misalin ƙarfe 5 na yamma a ranar Juma’a, jami’an RRS sun kama Sodiq Isa da Adekanmbi Ganiu bisa zargin yunkurin satar wayoyin hannu daga hannun fasinjoji a sassa daban-daban na Legas.