Malaman Bita na kananan hukumomin Jihar jigawa sun karrama Darakta Janar na Hukumar Jin dadin Alhazan jihar, Alhaji Ahmed Umar Labbo bisa nasarorin da aka samu a aikin hajjin bana.

 

A lokacin da jagoran Malaman Bitan yake jawabi wajen bikin karramawar da aka gudanar a shelkwatar hukumar dake Dutse babban birnin jihar, Ustaz Sa’idu Aliyu Galamawa ya bayyana cewar, makasudin karramawar shine ganin yadda Darakta Janar na hukumar ya bada gagurumar gudumawa wajen samun nasarar aikin hajjin 2025 a nan gida da kuma kasa mai tsarki.

 

Ya kara da cewar, sun karrama Labbo ne domin nuna godiya da kuma farin ciki da yadda aikin hajjin bana ya gudana a fannoni dabam dabam.

Shi kuwa Daraktan tsare-tsare na hukumar, Alhaji Muhammad Garba yayi nuni da cewar, wannan shine karon farko da malaman bita suka karrama wani shugaba a tarihin hukumar ta jigawan.

 

A jawabin sa, Darekta Janar na hukumar, Alhaji Ahmed Umar Labbo ya nuna farin cikin sa bisa wannan karramanci da malaman bitan suka yi ma shi.

 

Labbo, ya kuma ta’allaka nasarorin da aka samu a aikin hajjin bana akan hadin kai da goyan bayan Gwamna Umar Namadi.

Yana mai cewar, Gwamna Umar Namadi na sane da irin gudunmawar da malaman bita suka bayar wajen samun nasarar aikin hajjin bana.

 

Shima a na shi jawabin, Daraktan bincike da kididdiga na hukumar, Alhaji Arab Sabo Aujara ya godewa Malaman bitar bisa gudunmawar da suka bayar wajen samun nasarar aikin hajjin bana.

 

Usman Mohammed Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

NPA Ta Yi Wa Ma’aikatanta 1,500 Karin Girma

Dantsoho ya kara da cewa, nuna kwarewar ma’aikata na kara taimaka wa, wajen cimma burin da aka sanya a gaba, musamman a bangaren nuna yin gasa, a tafiyar da Tashohin Jiragen Ruwa.

“Ta irin wannan hanyar ce, za mu iya cimma bukatar da muke da ita da kuma cika muradin masu ruwa da tsaki, da ke a fannin, musamman domin mu kara karfafa karsashin ma’aikatan mu,” Inji Dantsoho.

Dantsoho ya kuma jinjinawa Minsitan ma’aikatar bunsa hada –hadar kasuwanci na kan Teku Adegboyega Oyetola, kan sahalewar Hukumar ta NPA, na yin karin girman ga ma’aikatan da suka amfana, wanda Hukumar ta jima, tana da bukatar yin hakan.

“Dole ne kuma in yabawa Ministanmu Adegboyega Oyetola, kan amincewar da ya yi, na kawo karshen batun yiwa ma’aikatan karin matsayin, ta hanyar gudanar masu da jarrabawar yin gwaji,” A cewar Shugaban.

A na sa jawabin madadin gamayyar kungiyoyin na Tashoshin Jiragen Ruwan kasar SSASCGOC, Kwamarade Bodunde, ya nuna jin dadinsa kan wannan karin matsayin da aka yiwa ma’aikatan.

“Muna kuma godiya, kan inganta walwalar ma’aikatan Hukumar ta NPA da kara inganta ayyukan ‘ya’yan kungiyar, musamman duba da irin yanayin matsin tattalin arzikin da ake fama da ita a kasar, Inji Bodunde.”

Shi kuwa, Janar Manaja a sashen tsare-tsare da samar da bayanai na Hukumar ta NPA Ikechukwu Onyemekara, ya bayyana cewa, zamanantar da kayan aikin Tashoshin Jiragen Ruwan kasar, hakan zai kara taimaka wa wajen kara inganta ayyukan ma’aikatan.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Tarayya Ta Karrama NPA Da Kyautar Gaskiya Da Riƙon Amana Ta 2025
  • Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna
  • NPA Ta Yi Wa Ma’aikatanta 1,500 Karin Girma
  • Aragchi: Kofar Iran Ta Tattaunawa A Bude Take, Amma Amurka Sai Ta Biya Kudade Kan Kura-Kuranta
  • Shugaban Kasar Iran Yace Huldar kasar Iran Da IAEA Zai Ci Gaba Ne Idan Ta Daina Fuska Biyu
  • Kwastam ta kama mazaƙutar jakai da aka yi yunƙurin safararsu
  • An gabatar da Ganduje a matsayin shugaban kwamitin hukumar FAAN
  • Tsohon Ɗan Takarar Gwamna A CPC, Haruna Sa’eed Kajuru, Ya Bukaci Gwamnatin Tarayya Ta Binciki Kisan ‘Yan Zariya  A Filato
  • Malaman firamare sun janye yajin aiki a Abuja