Malaman Jihar Jigawa Sun Karrama Shugaban Hukumar Alhazai Ta Jihar
Published: 11th, July 2025 GMT
Malaman Bita na kananan hukumomin Jihar jigawa sun karrama Darakta Janar na Hukumar Jin dadin Alhazan jihar, Alhaji Ahmed Umar Labbo bisa nasarorin da aka samu a aikin hajjin bana.
A lokacin da jagoran Malaman Bitan yake jawabi wajen bikin karramawar da aka gudanar a shelkwatar hukumar dake Dutse babban birnin jihar, Ustaz Sa’idu Aliyu Galamawa ya bayyana cewar, makasudin karramawar shine ganin yadda Darakta Janar na hukumar ya bada gagurumar gudumawa wajen samun nasarar aikin hajjin 2025 a nan gida da kuma kasa mai tsarki.
Ya kara da cewar, sun karrama Labbo ne domin nuna godiya da kuma farin ciki da yadda aikin hajjin bana ya gudana a fannoni dabam dabam.
Shi kuwa Daraktan tsare-tsare na hukumar, Alhaji Muhammad Garba yayi nuni da cewar, wannan shine karon farko da malaman bita suka karrama wani shugaba a tarihin hukumar ta jigawan.
A jawabin sa, Darekta Janar na hukumar, Alhaji Ahmed Umar Labbo ya nuna farin cikin sa bisa wannan karramanci da malaman bitan suka yi ma shi.
Labbo, ya kuma ta’allaka nasarorin da aka samu a aikin hajjin bana akan hadin kai da goyan bayan Gwamna Umar Namadi.
Yana mai cewar, Gwamna Umar Namadi na sane da irin gudunmawar da malaman bita suka bayar wajen samun nasarar aikin hajjin bana.
Shima a na shi jawabin, Daraktan bincike da kididdiga na hukumar, Alhaji Arab Sabo Aujara ya godewa Malaman bitar bisa gudunmawar da suka bayar wajen samun nasarar aikin hajjin bana.
Usman Mohammed Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa
এছাড়াও পড়ুন:
Ya Kamata Shugaba Tinubu Ya Ƙulla Alaƙa Ta Kut-da-kut Tsakanin Hukumar Shige Da Fice Da Kwastam – Babandede
“Iyakar kasa ba wai kawai yanki ne na tsaro ba. Yanki ne na al’adu; yanki ne na tarihi; haka nan ma yanki ne na tattalin arziki. Kula da shige da fice na da matukar amfani ga ci gabanmu. Wajibi ne Nijeriya ta zuba jari a kan kula da nau’in mutanen da take tacewa wajen shiga kasa da kuma irin mutanen da muke tacewa wajen fita daga kasa.
“Dole ne mu yi nazarin nau’in ayyukan da bakin-haure ke yi da kuma yadda suke shafar tattalin arzikinmu. Muna bukatar tsame mutanen da ke kawo cikas ga ci gabanmu”, in ji Babandede.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA