Fadar Shugaban Ƙasa ta ce yunƙurin da aka yi na haɗa waɗannan maganganun da abubuwan da suka faru a Jihar Ribas, musamman batun dakatar da Gwamna Siminalayi Fubara da ayyana dokar ta-baci, fassara ce da aka yi ta ba daidai ba, ko kuma suka ne ga kundin tsarin mulkin ƙasa.

“Domin kaucewa ruɗani, Shugaba Tinubu bai cire Gwamna Fubara daga mukaminsa ba,” sanarwar ta jaddada.

“Abin da aka aiwatar dokar dakatarwa ce, ba tsige wa ba. Wannan mataki da kuma ayyana dokar ta-baci an ɗauke su ne sakamakon rikicin siyasa mai tsanani da ya faru a Jihar Ribas a wancan lokacin.”

Sanarwar ta ce rikicin da ya faru a Ribas ya cika sharuɗɗan da kundin tsarin mulki ya gindaya na ɗaukar matakan gaggawa, bisa tanadin Sashe na 305(3)(c), wanda ke bayar da damar hakan idan an samu rashin zaman lafiya da tsaro a matsayin matakin da ya zama wajibi a yi amfani da shi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Fadar Shugaban Ƙasa

এছাড়াও পড়ুন:

Ana zargin takalar faɗa tsakanin fadar Aminu Ado da Sanusi II

Tashin hankali ya sake kunno kai a Masarautar Kano, inda aka zargi wasu magoya bayan Sarkin Kano na 15, Aminu Ado Bayero, da kutsawa cikin fadar Sarki Muhammadu Sanusi II ta Gidan Rumfa da ke Kofar Kudu.

Shaidu sun bayyana wa Aminiya cewa lamarin ya faru ne lokacin da tawagar Sarki Aminu ke dawowa daga gaisuwar rasuwar attajirin ɗan kasuwa, marigayi Alhaji Aminu Ɗantata.

Jami’an tsaro sun hallaka ’yan bindiga 30 a Katsina HOTUNA: Obi ya ziyarci iyalin Ɗantata don yi musu ta’aziyya

A wata sanarwa da kakakin masarautar Kano, Sadam Yakasai, ya fitar ya bayyana cewa Sarki Sanusi ba ya cikin fadar lokacin da abin ya faru ba.

“Sun fasa kofar shiga fadar, sun kai wa masu gadi hari, har suka raunata wasu.

“Haka kuma sun lalata motocin ‘yan sanda da ke wajen fadar. Aminu ya yi amfani da titin gidan Sarki maimakon ya bi hanyar Koki zuwa Nasarawa, inda yake zaune. Wannan ya nuna cewa da gangan ya nufi Gidan Rumfa.”

Yakasai, ya ƙara da cewa wannan ba shi ne karon farko da Sarki Aminu ke fakewa da hanyar Gidan Rumfa ba, yana jefa fargaba a zukatan mazauna unguwar.

Wani makusancin Sarki Sanusi, da ya nemi a sakaya sunansa ya ce harin ya faru ne da gozon bayan wasu daga cikin majalisar Sarki Aminu.

Ya ce wani bidiyo da ya karaɗe kafafen sada zumunta kafin tashin hankalin ya tabbatar da hakan, inda aka jiyo wani daga cikin majalisar yana tabbatar da abin da za su yi.

Tawagar Sarki Bayero ta musanta

Sai dai wani daga cikin tawagar Sarki Aminu Ado Bayero, Mukhtar Dahiru, ya ƙaryata zargin.

Ya ce: “Ni kaina ina cikin tawagar Sarki Aminu a lokacin. Mun dawo daga Koki ne bayan gaisuwar rasuwar Alhaji Aminu Ɗantata. Sai dai a kusa da fadar Ƙofar Kudu muka tarar da wasu ɓata-gari da suka rufe hanya ɗauke da muggan makamai.

“Masoya Sarki ne suka tunkare su domin su ba mu hanya mu wuce.”

Ya ƙara da cewa babu wani hari da suka kai wa jami’an tsaro a fadar Sarki Sanusi, sai dai ‘yan sanda ne suka yi amfani da barkonon tsohuwa domin shawo kan lamarin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar Da Shirin Ciyar Da Ɗalibai A Makarantun Zamfara
  • Malaman Jihar Jigawa Sun Karrama Shugaban Hukumar Alhazai Ta Jihar
  • Tinubu ne ya buɗe wa Buhari ƙofar zama shugaban ƙasa — Hadimi
  • Ba Tinubu kaɗai ne ya sa Buhari ya ci zaɓe a 2015 ba – Boss Mustapha
  • Ana zargin takalar faɗa tsakanin fadar Aminu Ado da Sanusi II
  • ’Yan ƙabilar Ibo ne suka fi aikata laifi a Jihar Anambra ba Fulani ba — Gwamna Soludo
  • Na Biya Bashin Garatutin Naira Biliyan 13.6 Da ’Yan Fanshon Zamfara Ke Bi Tun 2011 – Gwamna Lawal
  • An gabatar da Ganduje a matsayin shugaban kwamitin hukumar FAAN
  • Tsohon Ɗan Takarar Gwamna A CPC, Haruna Sa’eed Kajuru, Ya Bukaci Gwamnatin Tarayya Ta Binciki Kisan ‘Yan Zariya  A Filato