HausaTv:
2025-07-23@10:40:42 GMT

 Iran Ta Yi Kira Ga “FIFA” Da Ta Kori “Isra’ila” Daga Cikinta

Published: 22nd, July 2025 GMT

Kungiyar kwallon kafa ta Iran ta aike da sako zuwa ga hukumar kwallon kafa ta duniya da ta kori HKI daga cikinta

Shugaban kungiyar kwallon kafa ta Iran Mahdi Taj, ya bayyana cewa: Mun yi kira ga Sheikh Salman akan daukar kwakkwaran mataki akan ‘Yan Sahayoniya. Mun kuma rubuta wasika zuwa ga Fifa akan cewa ya zama wajibi a dagawa HKI jan kati.

 Bugu da kari, ya kuma ce; “Yan sahayoniya sun kai wa hukumar kwallon kafa ta Iran hari, ta kuma kashe mana alkalai, ‘yan wasa, don haka ya zama wajibi a kore su daga  Fifa.

 Taj ya kuma ce; Mun sami ci gaba sosai a wannan fagen, muna fatan kungiyar Fifa ta yi la’akari da wadannan laifukan na Isra’ila.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kwallon kafa ta

এছাড়াও পড়ুন:

 Kungiyar Malaman Musulmi Ta Yi Fatawar Wajabcin Kawo Karshen Killace Gaza

Kungiyar ta malaman musulumi ta fitar da fatawa da a ciki ta bukaci gwamnatoci da al’ummar musulmi da su yunkura cikin gaggawa domin kawo karshen killace yankin Gaza da aka yi, da kuma wajabcin kai musu abinci da magunguna.

Kungiyar malaman musulmin ta kuma bayyana abinda HKI take yi na killace mutanen Gaza fiye da miliyan biyu da haka su abinci da magani,musamman mata, yara da manya,wani babban laifi ne da ba shi da tamka a cikin tarihi, tana mai yin kira ga al’ummu da gwamnatoci da su motsa saboda su taimaki raunana.

Kwamitin fatawa da yake a karkashin wannan kungiyar ta malaman musulmi, ya dogara da ayoyin alkrur’ani da hadisan ma’aiki ( s.a.w) da manufofi na shari’a da ka’idoji na fikihu da su ka wajabta taimakawa wadanda aka zalunta da kawar da zaluncin da ake yi masa.

Fatawar ta kuma bayyana cewa, kin taimakawa wajen taimakawa alhali da akwai dama, yana daidai da yin tarayyar a cikin laifukan yaki.

A wani gefen, bayanin da ya fito daga kungiyar malaman musulmin ya kuma yi kira ga al’ummu da su fito domin yin zanga-zanga da zaman dirshan a gaban ofisoshin jakadancin kasashen Amurka da turai.

Har ila yau fatawar ta bukaci kasar Masar da ta dauki nauyin da ya rataya a wuyanta na tarihi da addini, ta bude mashigar Rafaha, saboda a shigar da kayan abinci da dukkanin bukatun yau da kullum. Har ila yau ta ce, yin shiru akan wannan batun shi ne;yin shiru akan wannan bala’in bai dace da ma’abota ilimi da addini.”

Wani bangare na sakon kungiyar ta malaman musulunci ya shafi yin kira ga ma’abota tunani da alkalami da su rika aikewa da sakwanni ta shafukansu domin yin matsyin lamba saboda a kawo karsehn wannan bala’in da yake faruwa a Gaza.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jami’an Kasashen Rasha, China, Iran Sun Gudanar Da Taron Hadin Gwiwa A Tehran
  •  Kungiyar Malaman Musulmi Ta Yi Fatawar Wajabcin Kawo Karshen Killace Gaza
  • Fizishkiyan: Batun Kare Hakkin Bil’adama Ba Komai Ba Ne Sai Karya
  • Majalisar Dattawa Za Ta Yi Zama Na Musamman Don Karrama Buhari 
  • Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
  • Tsoffin Jami’an ‘Yan Sanda Sun Bukaci A fitar Da Su Daga Cikin Shirin Fansho
  • MDD Ta Gargaɗi Isra’ila Kan Tilasta Wa Al’ummar Deir al-Balah Na Gaza Tashi
  • Jami’in Shari’ar Kasa Da Kasa Ya Bayyana Cewa: Harin Da Aka kai Kan Iran Babban Laifi Ne
  • Jaridar Washington Post Ta Ce; Yeman Ta Gurguta Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwan Isra’ila