Gwamnatin Borno ta bayyana yawan ma’aikata a matsayin dalilin da ya sanya ƙananan hukumomin jihar ba za su iya biyan mafi ƙarancin albashin ma’aikata na Naira dubu 70,000 ba.

Gwamnatin ta ce ta umarci shugabannin ƙananan hukumomin jihar su samar da tsari mai ɗorewa domin ƙaddamar da fara aikin mafi ƙarancin albashin.

WFP zai dakatar da tallafin abinci da kiwon lafiya a Nijeriya Matasa 3 sun rasu yayin wanka a rafi a Bauchi

Babban sakataren ma’aikatar kula da ƙananan hukumomi da masana’antu, Modu Alhaji cikin wata sanarwa da ya fitar ya ce yawan ma’aikatan ne ya haifar da jinkiri wajen fara biyan mafi ƙarancin albashin.

Modu ya yi bayanin cewa a wasu lokutan gwamnatin tarayya na turo ƙasa da Naira miliyan 700 zuwa asusun ƙananan hukumomin domin biyan albashin, a wani yanayi da ake buƙatar Naira miliyan 778 domin biyan ma’aikata albashi.

Gwamnatin ta yi nuni da cewa, Jihar Kano da ke da ƙananan hukumomi 44 na da ma’aikata dubu 30,000 ne kawai, amma Borno da ke da 27 na da ma’aikatan ƙananan hukumomi da yawansu ya kai dubu 90,000.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: jihar Borno Mafi ƙarancin albashi mafi ƙarancin

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Kano Ta Maida Gidan Marayu Zuwa Cibiyar Gyaran Mata Masu Shaye

Gwamnatin Jihar Kano ta kara zage damtse wajen farfado da mata masu shaye-shayen miyagun kwayoyi ta hanyar mayar da Cibiyar Gyaran Matan Gaya, wadda a da ya kasance gidan marayu, zuwa wurin gyaran tarbiya.

 

Kwamishiniyar harkokin mata, yara da masu bukata ta musamman, Hajiya Amina Abdullahi Sani, ta jagoranci wata babbar tawaga zuwa cibiyar da ke Gaya domin tantance bukatun gyare-gyare da kuma hada kai da ma’aikatu domin gudanar da aikin.

 

Tawagar ta hada da kwamishinan ayyuka Engr. Marwan Ahmad Badawi, tawagarsa ta fasaha, daraktoci, da mataimaka daga ma’aikatar harkokin mata.

 

A yayin ziyarar, kwamishinar ta bayyana wa takwararta na ma’aikatar ayyuka irin ayyukan da ake bukata domin inganta cibiyar, da suka hada da gyare-gyare da fadada gine-gine domin daukar da kuma gyaran tarbiyar mata masu shaye-shayen miyagun kwayoyi a cikin yanayi mai aminci da tallafi.

 

A nasa jawabin, kwamishinan ayyuka Eng. Marwan Badawi ya bayar da tabbacin cewa ma’aikatar ayyuka za ta hada kai da ma’aikatar harkokin mata domin bayar da tallafin fasaha da ababen more rayuwa.

 

“Za mu tabbatar da cewa wannan ginin ya cika ka’idojin da ake buƙata don tallafawa yadda ya kamata don farfado da matan mu da ke fama da shaye-shayen ƙwayoyi,”

 

Tawagar ta kuma kai ziyarar ban girma ga mai martaba Sarkin Gaya, inda suka sanar da shi shirin gwamnatin jihar na yin wannan hubbasa.

 

Sarkin ya bayyana goyon bayansa tare da yabawa Gwamna Abba Kabir Yusuf bisa yadda ya bayyana a matsayin jagoranci mai hangen nesa da tausayi.

 

Gwamnatin Gwamna Abba Kabir Yusuf ta ci gaba da jajircewa wajen baiwa masu karamin karfi tallafi tare da samar da yanayi mai kyau na farfadowa da sake dawo da mutanen da suke fama da shan miyagun kwayoyi musamman mata.

 

Rel/Khadijah Aliyu

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Yobe ta bada tallafi ga iyalan ’yan banga da suka rasu
  • Fiye Da  Falasdinawa 111 Ne Su Ka Yi Shahada Saboda Yunwa A Gaza
  • Yawan Ma’aikata Ne Ya Hana Borno Fara Biyan Sabon Mafi Ƙarancin Albashi – Zulum
  • Kotu Ta Umarci Gwamnatin Bauchi Ta Biya Tsohon Akanta-Janar Naira Miliyan 100
  • Gwamnatin Bauchi Ta Ƙaddamar Da Kwaskwarimar Majalisar Dokoki Kan Naira Biliyan 7
  •  Kungiyar Malaman Musulmi Ta Yi Fatawar Wajabcin Kawo Karshen Killace Gaza
  • UNICEF na zargin Gwamnatin Nijeriya da cin zarafin ƙananan yara
  • Gwamnatin Zamfara Ta Kira Babban Taron Tsaro Tare Da Bayyana Sabbin Dabaru Na Yakar ‘Yan Bindiga.
  • Gwamnatin Kano Ta Maida Gidan Marayu Zuwa Cibiyar Gyaran Mata Masu Shaye