Lavrov: Shuwagabannin Kasashen Yammacin Turai Suna Son Shiga Yaki Da Rasha
Published: 12th, July 2025 GMT
Ministan harkokin wajen kasar Rasha Sergey Lavrov ya ja kunnen shuwagabannin kasashen yammacin Turai kan shiga yaki da kasar Rasha.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto Lavrov yana fadar haka, a jiya Jumma’a. Ya kuma kara da cewa, labaran da suke isa kunnensa daga biranen Landan, Paris da kuma Berlin sun tabbatar masa da cewa, kasashen suna shirin yaki da kasar Rasha.
Ya ce, Rasha ta sha fadawa kasashen yammacin Turai, ci gaba da goyon bayan kasar Ukrai zai jawosu zuwa yaki da kasar Rasha.
Yaki wanda rabuwamma da irinsa tun bayan yakin duniya na II. Ya shay a sha fada masu kan cewa makaman da suke turawa Kiev daga karshe ba zai taba samar da zaman lafiya a yankin ba.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasar Rasha
এছাড়াও পড়ুন:
Qalibof: Asarorin HKI A Yakin Kwanaki 12 Yafi Abinda Ta Bayyana
shugaban majalisar dokokin kasar Iran Mohammad Baqir Qalibof ya bayyana cewa asarorin da HKI ta yi a yakin kwanaki 12 da JMI suna da yawa. Kuma babu shakka ya fi abinda ta bayyana.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto shugaban majalisar dokokin kasar ta Iran yana fadar haka a lokacinda yake hira da wata tashar talabijin a nan Tehran . Ya kuma kara da cewa. Maganar cewa uahudawa 3500 kawai suka ji rauni a yakim gaba daya karya ce.
Qalibof ya ce yana da tabbacin cewa yahudawa akalla 500 suna halaka sanadiyyar hare-haren da sojojin Iran suka kai a kan HKI a yankin kwamaki 12. .
Ya ce sojojin yahudawan sun saba boye yawan mutanen da suka halaka a yake-yaken da take fafatawa da masu gwagwarmaya a yankin. suna kuma hana yada hutunan bidyo na asarorin da suka yi a yaki. masili daga cikin wasu da dama shi ne yadda suka hada yar rahoton tashar talabijin ta Aljazeera daukar hotuna a yakin saboda basa son muatane su san gaskiya. su kuma ga irin yawan asarorin da suka yi.