Saura Kiris a Samin Tashin Gobarar Tankar Mai a Sakkwato
Published: 20th, March 2025 GMT
An dakile fashewar wata babbar tankar mai a Sokoto bayan da jami’an tsaro da jami’an kwana-kwana da masu bayar da agajin gaggawa suka yi gaggawar kai dauki bayan da tankar ta kife a hanyar Gagi-Nakasari a karamar hukumar Sokoto ta Kudu.
Wani shaidan gani da ido, Magaji Shanono ya shaidawa gidan rediyon Najeriya cewa tankar mai dauke da lita dubu arba’in da biyar na man fetur, ta wuntsila ne a lokacin da take kokarin shiga shatatalen Nakasari, inda ta zubar da mai.
Duk da cewa har zuwa lokacin hada wannan rahoto ba a fitar da wata sanarwa a hukumance ba, sakataren gwamnatin jihar Sokoto Muhammad Bello Sifawa ya halarci wurin da lamarin ya faru, domin ganin abin da ya faru.
Kwamishinan ‘yan sandan jihar Sokoto ya kuma sa ido kan matakan tsaro yayin da jami’an kashe gobara suka yi ta kokarin shawo kan lamarin.
Tawagar hadakar hukumar kashe gobara ta tarayya da ta jaha sun isa wurin da gaggawa, inda suka zuba kumfa don kawar da tururin wuta da hana tashin gobara a wajen.
Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta kasa NEMA da Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar SEMA su ma sun wajen don shawo kan cunkoson jama’a, da kuma dakile hadurruka.
Gidan Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa jami’an agajin gaggawa sun yi nasarar kwashe man zuwa wata tankar mai, inda suka kawar da illar zubewa ko fashewa.
Jami’an tsaro sun takaita zirga-zirga a wurin da lamarin ya faru, tare da hana mazauna wurin yunkurin diban mai.
NASIR MALALI
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
An kama ’yan bindiga 4 a Kano
An kama wasu mutum huɗu da ake zargin ’yan bindiga ne ɗauke da makamai da ake zaton bindigogi ne a tashar mota ta Ƙofar Ruwa da ke Jihar Kano.
Tashar motar, wadda ke kusa da kasuwar kayan gini ta Ƙofar Ruwa a Ƙaramar Hukumar Dala.
MAAUN: Ƙungiyar iyaye ta musanta zargin ƙara ƙudin yaye ɗalibai a jami’ar Sarkin Musulmi ya buƙaci gwamnonin Arewa suke saurarar ƙorafin jama’aA cewar mazauna yankin, an kama mutanen ne lokacin da suke ƙoƙarin shiga mota domin tafiya zuwa wani waje a cikin Kano.
“Mutanen da ke tashar motar ne suka lura da makaman da suke ɗauke da su. Take suka gaggauta sanar da jami’an tsaro, waɗanda suka kama su. Su huɗu ne gaba ɗaya,” in ji Musa Balarabe, wani mazaunin yankin.
Ya ce an kama su ne da misalin ƙarfe 1 na rana.
Da farko an kai su ofishin ’yan sanda na Ƙofar Ruwa, kafin daga bisani aka mayar da su ofishin Dala.
Wani mazaunin yankin, Umar Nuhu, ya ce yana cikin shagonsa da ke Kwanar Taya, kusa da ofishin ’yan sandan, lokacin da aka kawo mutanen.
Ya ce hakan ya jawo firgici, inda mutane suka fara gudu a ko’ina.
Nuhu, ya ƙara da cewa mutane da yawa sun yi dandazo a ofishin ’yan sandan, yayin da wasu matasan ke son ɗaukar doka a hannu.
Da aka tuntuɓi kakakin ’yan sandan Kano, Abdullahi Haruna Kiyawa, bai ce komai kan lamarin ba.
Ya ce har yanzu suna tattara bayanai kafin su fitar da sanarwa.
Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, babu wata sabuwar sanarwa daga rundunar ’yan sandan jihar.
Tashar Kofar Ruwa, tasha ce da ke jigilar fasinjoji zuwa jihohi irin su Katsina, Jigawa, Sakkwato, Zamfara, Kebbi, har ma da Jamhuriyar Nijar.
Wannan na zuwa ne daidai lokacin da Jihar Kano ke fama da hare-haren ’yan bindiga, musamman a yankunan da ke da iyaka da Jihar Katsina.