Saura Kiris a Samin Tashin Gobarar Tankar Mai a Sakkwato
Published: 20th, March 2025 GMT
An dakile fashewar wata babbar tankar mai a Sokoto bayan da jami’an tsaro da jami’an kwana-kwana da masu bayar da agajin gaggawa suka yi gaggawar kai dauki bayan da tankar ta kife a hanyar Gagi-Nakasari a karamar hukumar Sokoto ta Kudu.
Wani shaidan gani da ido, Magaji Shanono ya shaidawa gidan rediyon Najeriya cewa tankar mai dauke da lita dubu arba’in da biyar na man fetur, ta wuntsila ne a lokacin da take kokarin shiga shatatalen Nakasari, inda ta zubar da mai.
Duk da cewa har zuwa lokacin hada wannan rahoto ba a fitar da wata sanarwa a hukumance ba, sakataren gwamnatin jihar Sokoto Muhammad Bello Sifawa ya halarci wurin da lamarin ya faru, domin ganin abin da ya faru.
Kwamishinan ‘yan sandan jihar Sokoto ya kuma sa ido kan matakan tsaro yayin da jami’an kashe gobara suka yi ta kokarin shawo kan lamarin.
Tawagar hadakar hukumar kashe gobara ta tarayya da ta jaha sun isa wurin da gaggawa, inda suka zuba kumfa don kawar da tururin wuta da hana tashin gobara a wajen.
Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta kasa NEMA da Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar SEMA su ma sun wajen don shawo kan cunkoson jama’a, da kuma dakile hadurruka.
Gidan Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa jami’an agajin gaggawa sun yi nasarar kwashe man zuwa wata tankar mai, inda suka kawar da illar zubewa ko fashewa.
Jami’an tsaro sun takaita zirga-zirga a wurin da lamarin ya faru, tare da hana mazauna wurin yunkurin diban mai.
NASIR MALALI
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Tankin ruwa ya kashe mutum 4, wasu sun jikkata a Jigawa
An shiga jimami a garin Zugai da ke Ƙaramar Hukumar Roni ta Jihar Jigawa, bayan da wani tankin ruwa ya faɗo tare yin sanadin rasuwar mutum da jikkata wasu.
Daga cikin waɗanda suka rasu har da wata mace mai juna biyu.
An yanke wa shugaban ISWAP hukuncin ɗaurin shekara 20 a gidan yari Gwamna Abba ya gabatar da N1.36trn a matsayin kasafin 2026Majiyoyi sun bayyana cewa lamarin ya auku ne kwana uku bayan shugaban Ƙaramar Hukumar, ya raba ruwa ga masu sana’r sayar da ruwa, lamarin da ya haifar da ce-ce-ku-ce a tsakanin wasu mutane.
Tankin ruwa, wanda ke amfani da hasken rana wajen samar da ruwa, ya fashe yayin da mutane da yawa suka taru a ƙasa domin ɗibar ruwa.
Shaidu sun ce tankin ya rushe ba zato ba tsammani, inda mutum uku suka mutu nan take, waɗanda suka jikkata aka garzaya da su asibiti.
Shugaban Majalisar Ƙaramar Hukumar Roni, Dokta Abba Ya’u Roni, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya tabbatar da mutuwar mutum huɗu.
Dokta Abba, ya ce fashewar tankin ta faru ne sakamakon iska mai ƙarfi wadda ta turo tankin ya faɗo kan mutane.
Ya ƙara da cewa: “Na umarci mataimakina da jami’an majalisa su kai ziyara ƙauyen don tabbatar da cewa duk waɗanda suka ji rauni an kula da su.”