Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-11-26@17:40:48 GMT

Saura Kiris a Samin Tashin Gobarar Tankar Mai a Sakkwato

Published: 20th, March 2025 GMT

Saura Kiris a Samin Tashin Gobarar Tankar Mai a Sakkwato

An dakile fashewar wata babbar tankar mai a Sokoto bayan da jami’an tsaro da jami’an kwana-kwana da masu bayar da agajin gaggawa suka yi gaggawar kai dauki bayan da tankar ta kife a hanyar Gagi-Nakasari a karamar hukumar Sokoto ta Kudu.

 

Wani shaidan gani da ido, Magaji Shanono ya shaidawa gidan rediyon Najeriya cewa tankar mai dauke da lita dubu arba’in da biyar na man fetur, ta wuntsila ne a lokacin da take kokarin shiga shatatalen Nakasari, inda ta zubar da mai.

 

Duk da cewa har zuwa lokacin hada wannan rahoto ba a fitar da wata sanarwa a hukumance ba, sakataren gwamnatin jihar Sokoto Muhammad Bello Sifawa ya halarci wurin da lamarin ya faru, domin ganin abin da ya faru.

 

Kwamishinan ‘yan sandan jihar Sokoto ya kuma sa ido kan matakan tsaro yayin da jami’an kashe gobara suka yi ta kokarin shawo kan lamarin.

 

Tawagar hadakar hukumar kashe gobara ta tarayya da ta jaha sun isa wurin da gaggawa, inda suka zuba kumfa don kawar da tururin wuta da hana tashin gobara a wajen.

 

Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta kasa NEMA da Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar SEMA su ma sun wajen don shawo kan cunkoson jama’a, da kuma dakile hadurruka.

 

Gidan Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa jami’an agajin gaggawa sun yi nasarar kwashe man zuwa wata tankar mai, inda suka kawar da illar zubewa ko fashewa.

 

Jami’an tsaro sun takaita zirga-zirga a wurin da lamarin ya faru, tare da hana mazauna wurin yunkurin diban mai.

 

NASIR MALALI

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Gobara Sakkwato

এছাড়াও পড়ুন:

An sako ɗalibai 25 da ’yan bindiga suka sace a Kebbi

Rahotanni na cewa ɗalibai 25 da ’yan bindiga suka sace yayin harin da suka kai a Makarantar Sakandiren Mata da ke garin Maga a Jihar Kebbi sun shaƙi iskar ’yanci.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jami’an tsaro sun ƙaddamar da shirin murƙushe ’yan bindiga a Kaduna
  • An ceto ’yan mata 24 d aka yi garkuwa da su a makaranta a Kebbi
  • Tinubu Ya Nuna Farin Cikinsa Bisa Bayyanar Daliban Kebbi, Ya Bukaci a Ceto Sauran
  • Kano Pillars ta kawo ƙarshen wasanni 8 ba tare da nasara ba
  • An sako ɗalibai 25 da ’yan bindiga suka sace a Kebbi
  • ’Yan bindiga sun sace mutum 8 a Kano
  • Amarya ta yi wa angonta yankan rago bayan kwana 3 da aurensu a Katsina
  • Gobarar tankar mai ta ƙone gidaje a Jihar Neja
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 162
  • Tinubu Ya Janye ‘Yan Sanda Daga Tsaron Manyan Mutane, Ya Amince Da Daukar Sabbin 30,000