Ya kuma nuna jin daɗinsa da irin nasarorin da aka samu a ƙarƙashin jagorancin Kwamared Alhassan Yahayan, inda ya ce an ɗora ƙungiyar kan kyakkyawan turbar da ya kamata don ta ci gaba da taka rawar gani wajen bunƙasa aikin jarida a Nijeriya.

 

Yahaya ya jaddada cewa akwai kyakkyawar dangantaka tsakanin gwamnatin Jihar Gombe da ‘yan jarida, yana mai bada tabbacin cewa wannan kyakkyawar alaƙa da haɗin gwiwa za su kasance ginshiƙin gudanar da mulki a jihar.

 

“Mu a Jihar Gombe muna alfahari da daɗaɗɗiyar dangantakar da muka ƙulla da ‘yan jarida; ‘yan jarida abokan aikinmu ne masu ƙima a fagen kawo ci gaba, kuma muna ci gaba da jajircewa wajen ganin sun ci gaba da yin aiki a yanayin da zai bunƙasa sana’o’insu da ‘yancinsu,” inji Gwamna Inuwa Yahaya.

 

Ya kuma bada tabbacin cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da haɗa gwiwa da NUJ da sauran ƙungiyoyin yaɗa labarai don ba su damar ci gaba da kuma gudanar da muhimmiyar rawar da suke takawa wajen ankarar da gwamnati da wayar da kan jama’a.

 

Gwamna Inuwa ya ƙara da cewa, “Gudunmawar da kuka bayar na da matuƙar muhimmanci wajen inganta demokraɗiyya, da riƙon amana, da kuma shugabanci na gari a Nijeriya, muna godiya da irin rawar da kuke takawa wajen faɗakar da jama’a, da kare gaskiya, da kuma inganta manufofin gaskiya da adalci,” in ji Gwamna Inuwa Yahaya.

 

Ya kuma jaddada ƙudurin gwamnatin jihar na yin haɗin gwiwa mai ɗorewa da ‘yan jarida, inda ya jaddada muhimmancinsu wajen ci gaban Jihar Gombe dama Nijeriya baki ɗaya.

 

“Muna fatan ƙara ƙarfafa haɗin gwiwarmu da NUJ, kuma muna da yaƙinin cewa, tare, za mu ci gaba da gina ƙasa mai wadata, zaman lafiya da ci gaba,” in ji shi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Likitoci sun gindaya sabon sharaɗi bayan janye yajin aiki

Ƙungiyar Likitoci Masu Neman Ƙwarewa ta Najeriya (NARD) ta dakatar da yajin aikin da ta shafe kwanaki 29 tana yi, bayan wani taron gaggawa da Majalisar Koli ta ƙungiyar ta gudanar a ranar Asabar.

Shugaban NARD, Muhammad Suleiman, ya tabbatar da hakan a wata sanarwa da ya wallafa, inda ya bayyana cewa an dakatar da yajin aikin ne na tsawon makonni huɗu, domin bai wa gwamnatin Tarayya damar aiwatar da muhimman buƙatun da suka gabatar.

Dalilin da na koma jam’iyyar ADC — Atiku Kuɗin Cizo ya tilasta rufe fitacciyar sinima a Faransa

Ya ce an cimma matsayar ne bayan saka hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna (MoU) da ta ƙunshi ci gaban da aka samu kan manyan buƙatu 19 na ƙungiyar, ciki har da biyan bashin albashi da alawus-alawus da sauran haƙƙoƙinsu.

Suleiman ya ce Majalisar Koli ta dakatar da yajin aikin ne a matsayin wata alama ta kyakkyawan fata, domin a ci gaba da sa ido kan yadda gwamnati za ta aiwatar da alƙawuran.

Ya ƙara da cewa ƙungiyar za ta yi amfani da wannan wa’adi na makonni huɗu domin ƙara faɗakar da ’yan Najeriya da kuma ci gaba da tattaunawa da gwamnati.

Yajin aikin ƙungiyar ya bar asibitoci 91 cikin mawuyacin hali, kasancewar likitoci 11,500 — waɗanda su ne manyan ginshiƙai da ke kula da marasa lafiya a ƙasar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jagoran ‘Yan Democrat a Majalisar Dattawa: Trump Ba Shi da Ikon Kaddamar da Yaki Kan Venezuela
  • Sarkin Musulmi ya buƙaci gwamnonin Arewa suke saurarar ƙorafin jama’a
  • Najeriya Ta Kara Ƙaimi Wajen Kawar da Cutar HIV Nan da 2030
  • ‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Garin Eruka Na Jihar Kwara
  • Ministan Harkokin Wajen Turkiya Ya Isa Birnin Tehran Kuma Ya Gana Da Takwaransa Na Iran
  • Mataimakin Ministan Harkokin Wajen Kasar Saudiya Ya Gana Da Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran.
  • An Yi Ganawa A Tsakanin Ministocin Harkokin Wajen Turkiya
  • Likitoci sun gindaya sabon sharaɗi bayan janye yajin aiki
  • Muna buƙatar taimakon ƙasashen waje kan tsaro a Najeriya — Obasanjo
  • Yadda aka horar da mata 100 sana’o’in dogaro da kai a Gombe