Ya kuma nuna jin daɗinsa da irin nasarorin da aka samu a ƙarƙashin jagorancin Kwamared Alhassan Yahayan, inda ya ce an ɗora ƙungiyar kan kyakkyawan turbar da ya kamata don ta ci gaba da taka rawar gani wajen bunƙasa aikin jarida a Nijeriya.

 

Yahaya ya jaddada cewa akwai kyakkyawar dangantaka tsakanin gwamnatin Jihar Gombe da ‘yan jarida, yana mai bada tabbacin cewa wannan kyakkyawar alaƙa da haɗin gwiwa za su kasance ginshiƙin gudanar da mulki a jihar.

 

“Mu a Jihar Gombe muna alfahari da daɗaɗɗiyar dangantakar da muka ƙulla da ‘yan jarida; ‘yan jarida abokan aikinmu ne masu ƙima a fagen kawo ci gaba, kuma muna ci gaba da jajircewa wajen ganin sun ci gaba da yin aiki a yanayin da zai bunƙasa sana’o’insu da ‘yancinsu,” inji Gwamna Inuwa Yahaya.

 

Ya kuma bada tabbacin cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da haɗa gwiwa da NUJ da sauran ƙungiyoyin yaɗa labarai don ba su damar ci gaba da kuma gudanar da muhimmiyar rawar da suke takawa wajen ankarar da gwamnati da wayar da kan jama’a.

 

Gwamna Inuwa ya ƙara da cewa, “Gudunmawar da kuka bayar na da matuƙar muhimmanci wajen inganta demokraɗiyya, da riƙon amana, da kuma shugabanci na gari a Nijeriya, muna godiya da irin rawar da kuke takawa wajen faɗakar da jama’a, da kare gaskiya, da kuma inganta manufofin gaskiya da adalci,” in ji Gwamna Inuwa Yahaya.

 

Ya kuma jaddada ƙudurin gwamnatin jihar na yin haɗin gwiwa mai ɗorewa da ‘yan jarida, inda ya jaddada muhimmancinsu wajen ci gaban Jihar Gombe dama Nijeriya baki ɗaya.

 

“Muna fatan ƙara ƙarfafa haɗin gwiwarmu da NUJ, kuma muna da yaƙinin cewa, tare, za mu ci gaba da gina ƙasa mai wadata, zaman lafiya da ci gaba,” in ji shi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Kukan al’umma kan lalacewar hanyar Dukku

Al’ummar garin Dukku a Ƙaramar Hukumar Dukku ta Jihar Gombe sun koka kan mummunan halin hanyar da ta haɗa su da babban birnin jihar, tare da kira ga gwamnati da ta gaggauta gyaran ta.

A cewar direbobi, tafiyar Dukku zuwa Gombe wadda a da take ɗaukar mintuna 50 kacal, yanzu ta koma fiye da awa biyu saboda lalacewar hanyar, abin da ke jawo gajiya da takaici ga fasinjoji da masu tuƙi.

An fara gina hanyar Gombe-Dukku-Darazo ne tun a shekarun 1980, aka gyara ta a farkon shekarun 2000. Sai dai daga baya aka yi sakaci da ita duk da kasancewarta hanyar da matafiya daga jihohin Adamawa, Taraba, Jigawa, Kano, Bauchi da wasu ke bi.

“Gyaran motoci na cinye mana kuɗi”

Usman Abubakar, direba mai shekaru 45 da gogewar tuki na sama da shekaru 19, ya ce lalacewar hanyar na sa direbobi kashe kuɗi masu yawa wajen gyaran motoci.

Bida Poly ta sa sojoji kula da jarrabawar ɗalibai ’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu

“Gaskiya hanyar ta lalace matuƙa. A da tafiyar Dukku zuwa Gombe kan ɗauki mintuna 45, yanzu kuwa ko awa biyu ba ta isa ba. Rami ne a ko’ina, musamman daga Tongoyel zuwa Bojude da Bozonshulwa. Sau da dama idan ka fito da safe sai ka tarar da motoci sun tsaya cak a hanya. Shock absorber, gilashi da sauran sassan mota suna yawan lalacewa saboda ramukan hanyar,” in ji shi.

Ya ce a da ‘shock absorber’ na iya kaiwa shekara biyu kafin ya lalace, amma yanzu ko watanni uku bai yi ba sai ya karye. Hakazalika tsohon gilashi da ake siya ₦90,000 yanzu cikin sati biyu kawai sai ya fashe.

Usman ya kuma ce ya sha yin haɗura a hanyar cikin watanni biyu kacal, inda tayar motarsa ta fashe, ‘shock absorber’ ya karye, sannan kingpin ya lalace — duka sakamakon shiga ramuka.

Wani direba, Abubakar Hassan, ya ce lalacewar hanyar ta kai shi ga tunanin barin aikin tuƙi gaba ɗaya saboda asarar kuɗi.

“Idan ruwan sama ya sauka, tafiya sai ta koma tamkar azaba. Sau da dama motoci kan kwana a hanya saboda lalacewa,” in ji shi.

Fasinjoji sun bayyana ƙalubale

Kabiru Zubairu, ɗaya daga cikin fasinjojin da ke yawan amfani da hanyar, ya ce, “A da tafiyar kilomita 72 kan ɗauki mintuna 45 zuwa 60, yanzu ta koma awa biyu. Idan na taso Dukku da karfe 7:00 na safe, yanzu sai mu isa bayan 9:00. Wannan na jawo mana jinkiri sosai.”

Wani fasinja, Abubakar Aliyu, ya ce mutane da dama sun daina zuwa Gombe saboda halin hanyar. “Idan ka yi tafiya sai jikinka ya yi ciwo. Wasu matasa kan zuba yashi a cikin ramuka, amma ruwan sama yana wanke shi,” in ji shi.

Muhimmancin hanyar — Masana

Mai sharhi a harkokin jama’a, Sulaiman Sa’idu Liman, ya ce kusan kilomita 64 daga cikin 72 na hanyar Dukku zuwa Gombe sun lalace, kuma motoci yanzu ba sa iya wuce gudu na kilomita 20 a awa ɗaya.

“Hanyar na da muhimmanci ga tattalin arziki da walwalar al’umma. Ana jigilar kayan gona, kayayyakin lafiya da marasa lafiya ta wannan hanya zuwa Asibitin Koyarwa na Tarayya (FTH) Gombe,” in ji shi.

Likita Aliyu Bashir kuwa ya ce lalacewar hanyar na haifar da matsaloli ga lafiyar jama’a, musamman ƙura da ke haddasa cutar asma, da kuma haɗarin haihuwa kafin lokaci ga mata masu juna biyu saboda girgizar mota.

Kungiyoyi da direbobi sun yi kira

Shugaban Ƙungiyar Tuntuɓa ta Dukku (DCF), Muhammad Bala Hashidu, ya yi kira da a gaggauta gyaran hanyar gaba ɗaya.

Shi ma shugaban Kungiyar Direbobi ta NURTW a Dukku, Abdulhamid Hassan, ya ce kusan kowace rana ana samun aƙalla motoci 10 da ke lalacewa a kan hanyar, abin da ya rage musu kuɗin shiga.

Gwamnati ta magantu

Mai magana da yawun gwamnan Gombe, Ismaila Uba Misilli, ya tabbatar da cewa gwamnati na aiki tare da takwarorinta na Arewa maso Gabas domin samun tallafin Gwamnatin Tarayya wajen gyaran hanyar.

“Kwanan nan gwamnonin yankin sun gana da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu inda suka roƙi a gyara muhimman hanyoyi ciki har da wannan. Domin hanya ta tarayya ce, gwamnatocin jihohi ba su da ikon gyaran ta kai tsaye. Amma gwamnoni sun dage wajen ganin an gyara ta,” in ji shi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja
  • Gwamnati ta ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani 20 a Sakkwato
  • Iran Ta Gabatar Da Sabbin Kayayyaki Guda 5 A Wajen Taron Kolin kere-kere .
  • Kukan al’umma kan lalacewar hanyar Dukku
  • Pezeshkian: Saudiyya Na Iya Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Samar Da Hadin Kan Kasashen Musulmi
  • Kungiyar Human Rights Watch; Isra’ila Ta Kashe ‘Yan Jarida Fiye Da 30 A Kasar Yemen Ne Da Gangan  
  • Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa
  • Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta
  • Dole sai mun tantance wa’azi kafin a yi —Gwamnan Neja
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Qatar, Turkiyya, Pakistan Da Labanon A Doha