Ya kuma nuna jin daɗinsa da irin nasarorin da aka samu a ƙarƙashin jagorancin Kwamared Alhassan Yahayan, inda ya ce an ɗora ƙungiyar kan kyakkyawan turbar da ya kamata don ta ci gaba da taka rawar gani wajen bunƙasa aikin jarida a Nijeriya.

 

Yahaya ya jaddada cewa akwai kyakkyawar dangantaka tsakanin gwamnatin Jihar Gombe da ‘yan jarida, yana mai bada tabbacin cewa wannan kyakkyawar alaƙa da haɗin gwiwa za su kasance ginshiƙin gudanar da mulki a jihar.

 

“Mu a Jihar Gombe muna alfahari da daɗaɗɗiyar dangantakar da muka ƙulla da ‘yan jarida; ‘yan jarida abokan aikinmu ne masu ƙima a fagen kawo ci gaba, kuma muna ci gaba da jajircewa wajen ganin sun ci gaba da yin aiki a yanayin da zai bunƙasa sana’o’insu da ‘yancinsu,” inji Gwamna Inuwa Yahaya.

 

Ya kuma bada tabbacin cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da haɗa gwiwa da NUJ da sauran ƙungiyoyin yaɗa labarai don ba su damar ci gaba da kuma gudanar da muhimmiyar rawar da suke takawa wajen ankarar da gwamnati da wayar da kan jama’a.

 

Gwamna Inuwa ya ƙara da cewa, “Gudunmawar da kuka bayar na da matuƙar muhimmanci wajen inganta demokraɗiyya, da riƙon amana, da kuma shugabanci na gari a Nijeriya, muna godiya da irin rawar da kuke takawa wajen faɗakar da jama’a, da kare gaskiya, da kuma inganta manufofin gaskiya da adalci,” in ji Gwamna Inuwa Yahaya.

 

Ya kuma jaddada ƙudurin gwamnatin jihar na yin haɗin gwiwa mai ɗorewa da ‘yan jarida, inda ya jaddada muhimmancinsu wajen ci gaban Jihar Gombe dama Nijeriya baki ɗaya.

 

“Muna fatan ƙara ƙarfafa haɗin gwiwarmu da NUJ, kuma muna da yaƙinin cewa, tare, za mu ci gaba da gina ƙasa mai wadata, zaman lafiya da ci gaba,” in ji shi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Yobe ta ba da umarnin rufe makarantun kwana a jihar

Gwamnatin Jihar Yobe, ta bayar da umarnin rufe dukkanin makarantun kwana a jihar domin kare ɗalibai, biyo bayan taɓarɓarewar rashin tsaro a wasu jihohin ƙasar nan.

Wannan na cikin wata sanarwa da daraktan yaɗa labarai na gwamnan jihar, Mamman Mohammed, ya fitar a ranar Asabar.

Matsalar tsaro a Arewa na damuna matuƙa — Tinubu Atiku ya nemi a ayyana dokar ta-ɓaci kan satar ɗalibai a Najeriya

Ya bayyana cewa an yanke wannan mataki ne bayan taro kan sha’anin tsaro da Gwamna Mai Mala Buni ya yi tare da hukumomin tsaro, inda suka yi nazari kan barazanar da makarantu ke fuskanta a jihar.

Sanarwar, wacce sakataren dindindin na ma’aikatar ilimi, Dokta Bukar, ya sanya wa hannu, ta ce an rufe makarantun kwana nan take har sai al’amura sun daidaita.

Gwamna Buni, ya roki jama’ar jihar da su ci gaba da yin addu’a domin samun zaman lafiya, inda kuma ya tabbatar da cewa gwamnati tana ɗaukar matakai don kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

Wannan mataki na zuwa ne biyo bayan sace ɗalibai da ’yan bindiga suka yi a jihohin Kebbi da Neja.

Yanzu dai matsalar na ci gaba da tayar da hankalin jama’a a Najeriya, inda mutane da dama ke kiran gwamnati da ta ɗauki matakin gaggawa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tsaron makarantu: ’Yan Sanda da Shugabannin Makarantu sun tsara sabbin matakai a Gombe
  • Gwamna Namadi Ya Kaddamar da Titi Mai Tsawon Kilomita 13 a ‘Yankwashi
  • Amnesty International Ta Zargi Najeriya Da Gazawa Wajen Kare Rayukan Al’ummarta
  • Wakilin MDD Ya Bukaci Goyon Bayan Iran Wajen Tabbatar Da Zaman Lafiya A Yamen
  • An rufe duk makarantu a Jihar Bauchi saboda matsalar tsaro
  • Najeriya Ta Cimma Sabon Tsarin Hadin Gwiwa Kan Sha’anin Tsaro da Amurka
  • Habasha: Bayan Shekaru 10,000 Dutsen Hayli Gubbi Ya Yi Aman Wuta
  • An rufe duk makarantu a Jihar Bauchi na saboda matsalar tsaro
  • ’Yan sanda sun ƙaryata jita-jitar kai wa coci hari a Gombe
  • Gwamnatin Yobe ta ba da umarnin rufe makarantun kwana a jihar