Cikar NUJ Shekaru 70: ‘Yan Jarida Abokan Hulɗa Ne Wajen Aza Kyakkyawar Makoma – Gwamnan Gombe
Published: 20th, March 2025 GMT
Ya kuma nuna jin daɗinsa da irin nasarorin da aka samu a ƙarƙashin jagorancin Kwamared Alhassan Yahayan, inda ya ce an ɗora ƙungiyar kan kyakkyawan turbar da ya kamata don ta ci gaba da taka rawar gani wajen bunƙasa aikin jarida a Nijeriya.
Yahaya ya jaddada cewa akwai kyakkyawar dangantaka tsakanin gwamnatin Jihar Gombe da ‘yan jarida, yana mai bada tabbacin cewa wannan kyakkyawar alaƙa da haɗin gwiwa za su kasance ginshiƙin gudanar da mulki a jihar.
“Mu a Jihar Gombe muna alfahari da daɗaɗɗiyar dangantakar da muka ƙulla da ‘yan jarida; ‘yan jarida abokan aikinmu ne masu ƙima a fagen kawo ci gaba, kuma muna ci gaba da jajircewa wajen ganin sun ci gaba da yin aiki a yanayin da zai bunƙasa sana’o’insu da ‘yancinsu,” inji Gwamna Inuwa Yahaya.
Ya kuma bada tabbacin cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da haɗa gwiwa da NUJ da sauran ƙungiyoyin yaɗa labarai don ba su damar ci gaba da kuma gudanar da muhimmiyar rawar da suke takawa wajen ankarar da gwamnati da wayar da kan jama’a.
Gwamna Inuwa ya ƙara da cewa, “Gudunmawar da kuka bayar na da matuƙar muhimmanci wajen inganta demokraɗiyya, da riƙon amana, da kuma shugabanci na gari a Nijeriya, muna godiya da irin rawar da kuke takawa wajen faɗakar da jama’a, da kare gaskiya, da kuma inganta manufofin gaskiya da adalci,” in ji Gwamna Inuwa Yahaya.
Ya kuma jaddada ƙudurin gwamnatin jihar na yin haɗin gwiwa mai ɗorewa da ‘yan jarida, inda ya jaddada muhimmancinsu wajen ci gaban Jihar Gombe dama Nijeriya baki ɗaya.
“Muna fatan ƙara ƙarfafa haɗin gwiwarmu da NUJ, kuma muna da yaƙinin cewa, tare, za mu ci gaba da gina ƙasa mai wadata, zaman lafiya da ci gaba,” in ji shi.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Kula Da Lafiya A Matakin Farko: Zamfara Ta Yin Fintinƙau
Sanarwar ta Sulaiman ta ƙara da cewa, asusun cibiyar ya mayar da hankali ne wajen ingantawa tare da samar da isassun kuɗaɗe don ƙarfafa wa jihohi 36 wajen samar da kula da lafiya a matakin farko mai aminci da inganci.
Sanarwar ta ce, “Jihar Zamfara ta sami kyautar Dalar Amurka 500,000 a matsayin wacce ta zama zakara a yankin Arewa maso Yamma wajen kula da cibiyoyin kula da lafiya a matakin farko.
“Wannan karramawa da aka miƙa wa Gwamna Dauda Lawal, tallafi ne na haɗin gwiwa tsakanin ‘Bill and Melinda Gates Foundation, United Nations International Children’s Emergency Fund (UNICEF), Dangote Foundation da National Primary Healthcare Development Agency (NPHCDA).’
“Wannan karramawa, ta nuna a fili cewa ayyana dokar ta-baci da Gwamna Lawal ya yi wa fannin kula da lafiya, abin yana haifar da makamako mai kyau da aka tsammata.
“Zamfara da sauran jihohin da suka yi zarra a wannan fanni daga yankunan Arewa maso Gabas, Arewa ta Tsakiya, Kudu maso Yamma, Kudu maso Gabas da Kudu maso Kudu, duk sum raba kuɗi Dalar Amurka Miliyan 6.1 a karo na uku na wannan karramawa.”
ShareTweetSendShare MASU ALAKA