Ya kuma nuna jin daɗinsa da irin nasarorin da aka samu a ƙarƙashin jagorancin Kwamared Alhassan Yahayan, inda ya ce an ɗora ƙungiyar kan kyakkyawan turbar da ya kamata don ta ci gaba da taka rawar gani wajen bunƙasa aikin jarida a Nijeriya.

 

Yahaya ya jaddada cewa akwai kyakkyawar dangantaka tsakanin gwamnatin Jihar Gombe da ‘yan jarida, yana mai bada tabbacin cewa wannan kyakkyawar alaƙa da haɗin gwiwa za su kasance ginshiƙin gudanar da mulki a jihar.

 

“Mu a Jihar Gombe muna alfahari da daɗaɗɗiyar dangantakar da muka ƙulla da ‘yan jarida; ‘yan jarida abokan aikinmu ne masu ƙima a fagen kawo ci gaba, kuma muna ci gaba da jajircewa wajen ganin sun ci gaba da yin aiki a yanayin da zai bunƙasa sana’o’insu da ‘yancinsu,” inji Gwamna Inuwa Yahaya.

 

Ya kuma bada tabbacin cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da haɗa gwiwa da NUJ da sauran ƙungiyoyin yaɗa labarai don ba su damar ci gaba da kuma gudanar da muhimmiyar rawar da suke takawa wajen ankarar da gwamnati da wayar da kan jama’a.

 

Gwamna Inuwa ya ƙara da cewa, “Gudunmawar da kuka bayar na da matuƙar muhimmanci wajen inganta demokraɗiyya, da riƙon amana, da kuma shugabanci na gari a Nijeriya, muna godiya da irin rawar da kuke takawa wajen faɗakar da jama’a, da kare gaskiya, da kuma inganta manufofin gaskiya da adalci,” in ji Gwamna Inuwa Yahaya.

 

Ya kuma jaddada ƙudurin gwamnatin jihar na yin haɗin gwiwa mai ɗorewa da ‘yan jarida, inda ya jaddada muhimmancinsu wajen ci gaban Jihar Gombe dama Nijeriya baki ɗaya.

 

“Muna fatan ƙara ƙarfafa haɗin gwiwarmu da NUJ, kuma muna da yaƙinin cewa, tare, za mu ci gaba da gina ƙasa mai wadata, zaman lafiya da ci gaba,” in ji shi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

An janye ’yan sanda 11,566 daga yi wa manyan mutane rakiya – Egbetokun

Babban Sufeton ’yan sandan Najeriya, Kayode Egbetokun, ya ce sun janye ’yan sanda 11,566 da ke rakiyar manyan mutane kamar yadda Shugaban Ƙasa ya ba da umarni a kwanakin baya.

Ya kuma ce an sake tura waɗannan jami’an zuwa muhimman wuraren da aka fi buƙatars su don kare al’ummomi masu rauni a fadin ƙasa.

NAJERIYA A YAU:Waiwaye Kan Irin Gudunmawar Da Sheikh Dahiru Bauci Ya Bayar Ga Cigaban Addini An gano gawawwakin mata uku ’yan Kamaru da aka sace a Anambra

Aminiya ta rawaito cewa Shugaba Bola Tinubu, a ranar Lahadi, ya bayar da umarnin janye jami’an ‘yan sanda daga aikin tsaron manyan mutane tare da umartar a sake tura su zuwa ayyukan tsaro na asali.

Umarnin ya biyo bayan taron tsaro da aka gudanar a Abuja tare da shugabannin rundunonin tsaro da shugaban hukumar tsaro ta DSS.

Yayin da yake jawabi a hedikwatar ’yan sanda da ke Abuja, ranar Alhamis, lokacin da ya gana da manyan jami’an ‘yan sanda masu mukamin kwamishina, Egbetokun ya ce jami’an da aka janye za a mayar da su ga ayyukan tsaro na asali.

Ya ce shawarar janye jami’an daga aikin tsaron mutanen ba ta samo asali daga son rai ba, sai dai daga bukatar gaggawa ta karkatar da ma’aikata zuwa wuraren da tsaron jama’a ya fi bukata.

A cewarsa, wannan mataki ya yi daidai da babban aikin Hukumar ‘Yan Sanda ta Najeriya, wato kare ‘yan ƙasa, al’ummomi da kuma tabbatar da zaman lafiya, yana mai jaddada cewa dukkan jami’an 11,566 da aka janye an sake tura su wuraren aiki.

“A bisa umarnin Shugaban Ƙasa, mun janye jami’an 11,566 daga aikin tsaron manyan mutane. Waɗannan jami’an za a sake tura su zuwa muhimman ayyukan tsaro nan take,” in ji shi.

Babban Sufeton ya ce janyewar za ta bai wa ‘yan sanda damar ƙara yawan jami’an da za su yi aiki wajen tsaron ƙauyuka da birane, kare jama’a da yawa, ƙarfafa sintiri, ayyukan tsaro bisa bayanan sirri, da kuma daƙile barazanar tsaro cikin gaggawa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Yi Ganawa A Tsakanin Ministocin Harkokin Wajen Turkiya
  • Muna buƙatar taimakon ƙasashen waje kan tsaro a Najeriya — Obasanjo
  • Yadda aka horar da mata 100 sana’o’in dogaro da kai a Gombe
  • Ziyarar Da Larijani Ya Kai Pakistan Ta Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Kara Dankon Zumunci
  • Sarakuna sun goyi bayan Gwamnatin Gombe kan yaƙi da cin zarafin mata
  • Asibitin Kula Da Masu Lalurar Ƙwaƙwalwa Na Kaduna Na Bunƙasa Ta Fannoni Daban-Daban
  • Portugal ta lashe Kofin Duniya na ’yan ƙasa da shekaru 17 a karon farko
  • Yadda mutane suka yi cikar ƙwari don halartar jana’izar Sheikh Dahiru Bauchi
  • Ya kamata ’yan majalisar Najeriya su koma zaman wucin gadi – Ndume
  • An janye ’yan sanda 11,566 daga yi wa manyan mutane rakiya – Egbetokun