Sojoji Sun Ceto Mutanen Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Katsina Da Zamfara
Published: 20th, March 2025 GMT
Dakarun Sashe na 2 tare da hadin gwiwar sojojin sama na rundunar hadin gwiwa ta Operation Fansan Yamma sun ceto mutane 101 da aka yi garkuwa da su a fadin Kankara a jihar Katsina da Shinkafi a jihar Zamfara a ranakun 17 da 18 ga watan Maris 2025.
A cewar sanarwar mai Magana da aywun rundunar Fansan Yamma, Laftanar Kanar Abubukar Abdullahi ya bayyana cewa, a yayin farmakin an kashe ‘yan ta’adda 10 a wata arangama da suka yi a gundumar Faru da ke karamar hukumar Maradun.
Ta ce an fara kai farmakin ne a jihar Katsina, inda sojoji suka kai farmakin a kan ‘yan ta’addan a babbar filin Pauwa da ke karamar hukumar Kankara.
“Hakan ya yi sanadin kashe ‘yan ta’adda 3 tare da ceto mutane 84 da aka yi garkuwa da su.
A halin da ake ciki kuma, a jihar Zamfara, sojojin sun aiwatar da wasu ayyuka a yankin Bagabuzu da ke gundumar Faru, cikin karamar hukumar Maradun wanda ya kai ga halaka ‘yan ta’adda 7 tare da kwato babur da dai sauransu.
Bugu da kari, an yi nasarar ceto mutane 17 da wani sarkin ‘yan ta’adda ya yi garkuwa da su daga kauyukan Tsibiri da Doka da ke karamar hukumar Shinkafi, kuma a halin yanzu suna samun kulawar likitoci a wani asibiti da ke yankin.
Sanarwar ta bayyana cewa, Operation Fansan Yamma na ci gaba da jajircewa wajen tabbatar da tsaron al’ummar jihohin Katsina da Zamfara.
REL/AMINU DALHATU
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Fansar Yamma Zamfara karamar hukumar yan ta adda
এছাড়াও পড়ুন:
An Yaba Ma Iyaye Bisa Goyon Bayansu ga Shirin Rigakafin Shan Inna a Karamar Hukumar Ringim
Kananan yara sama da 93,200 ne ake sa ran yiwa allurar rigakafin cutar shan Inna da ake gudanarwa a Karamar Hukumar Ringim ta Jihar Jigawa.
Kazalika, kananan yara sama da 53,800 ne ake sa ran digawa sinadarin vitamin A a yankin.
Shugaban hukumar lafiya matakin farko na yankin Aminu Abubakar Kwandiko ya yaba da yadda iyaye ke bada hadin kai da goyan baya ga shirin.
Ya kuma ja hankalin ma’aikatan rigakafin da su sanya kishi da kwazo wajen samun nasarar aikin.
A sakon da ya aike da shi a taron tattara bayanan aikin rigakafi na yankin, Shugaban Karamar Hukumar, Mallam Badamasi Garba Dabi ya jaddada kudirin Karamar Hukumar na ci gaba da bada gudunmuwa wajen samun nasarar shirin rigakafin.