Dakarun Sashe na 2 tare da hadin gwiwar sojojin sama na rundunar hadin gwiwa ta Operation Fansan Yamma sun ceto mutane 101 da aka yi garkuwa da su a fadin Kankara a jihar Katsina da Shinkafi a jihar Zamfara a ranakun 17 da 18 ga watan Maris 2025.

 

A cewar sanarwar mai Magana da aywun rundunar Fansan Yamma, Laftanar Kanar Abubukar Abdullahi ya bayyana cewa, a yayin farmakin an kashe ‘yan ta’adda 10 a wata arangama da suka yi a gundumar Faru da ke karamar hukumar Maradun.

 

Ta ce an fara kai farmakin ne a jihar Katsina, inda sojoji suka kai farmakin a kan ‘yan ta’addan a babbar filin Pauwa da ke karamar hukumar Kankara.

 

“Hakan ya yi sanadin kashe ‘yan ta’adda 3 tare da ceto mutane 84 da aka yi garkuwa da su.

 

A halin da ake ciki kuma, a jihar Zamfara, sojojin sun aiwatar da wasu ayyuka a yankin Bagabuzu da ke gundumar Faru, cikin karamar hukumar Maradun wanda ya kai ga halaka ‘yan ta’adda 7 tare da kwato babur da dai sauransu.

 

Bugu da kari, an yi nasarar ceto mutane 17 da wani sarkin ‘yan ta’adda ya yi garkuwa da su daga kauyukan Tsibiri da Doka da ke karamar hukumar Shinkafi, kuma a halin yanzu suna samun kulawar likitoci a wani asibiti da ke yankin.

 

Sanarwar ta bayyana cewa, Operation Fansan Yamma na ci gaba da jajircewa wajen tabbatar da tsaron al’ummar jihohin Katsina da Zamfara.

 

REL/AMINU DALHATU

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Fansar Yamma Zamfara karamar hukumar yan ta adda

এছাড়াও পড়ুন:

An Yaba Ma Iyaye Bisa Goyon Bayansu ga Shirin Rigakafin Shan Inna a Karamar Hukumar Ringim

Kananan yara sama da 93,200 ne ake sa ran yiwa allurar rigakafin cutar shan Inna da ake gudanarwa a Karamar Hukumar Ringim ta Jihar Jigawa.

Kazalika, kananan yara sama da 53,800 ne ake sa ran digawa sinadarin vitamin A a yankin.

Shugaban hukumar lafiya matakin farko na yankin Aminu Abubakar Kwandiko ya yaba da yadda iyaye ke bada hadin kai da goyan baya ga shirin.

Ya kuma ja hankalin ma’aikatan rigakafin da su sanya kishi da kwazo wajen samun nasarar aikin.

A sakon da ya aike da shi a taron tattara bayanan aikin rigakafi na yankin, Shugaban Karamar Hukumar, Mallam Badamasi Garba Dabi ya jaddada kudirin Karamar Hukumar na ci gaba da bada gudunmuwa wajen samun nasarar shirin rigakafin.

 

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Sha Alwashin Wadata Al’ummarsa da Tsaftataccen Ruwan Sha
  • Hukumar Karɓar Ƙorafe-ƙorafe ta Jigawa Ta Nemi Kotuna Su Daina Jan Kafa Wajen Aiwatar da Shari’a
  • Zanga-zanga ta ɓarke kan zargin sojoji da kashe mata a Adamawa
  • Rikicin Iyakar Thailand da Cambodia Ya Tilasta wa Dubban Mutane Barin Muhallansu
  • Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara Ta Taya Oluremi Tinubu Murnar Nadin Sarauta a Ile-Ife
  • An Yaba Ma Iyaye Bisa Goyon Bayansu ga Shirin Rigakafin Shan Inna a Karamar Hukumar Ringim
  • Za a Yi wa Yara 194,000 Rigakafin Cutar Shan Inna a Karamar Hukumar Birnin Kudu
  • An dakatar da Shugaban Karamar Hukumar Lafia
  • Zaben 2027: NNPP Ta Sha Alwashin Maye Gurbin Tinubu da Radda
  • Sojoji sun kashe ’yan bindiga 13, sun ceto ’yan kasuwa a Sakkwato