Sojoji Sun Ceto Mutanen Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Katsina Da Zamfara
Published: 20th, March 2025 GMT
Dakarun Sashe na 2 tare da hadin gwiwar sojojin sama na rundunar hadin gwiwa ta Operation Fansan Yamma sun ceto mutane 101 da aka yi garkuwa da su a fadin Kankara a jihar Katsina da Shinkafi a jihar Zamfara a ranakun 17 da 18 ga watan Maris 2025.
A cewar sanarwar mai Magana da aywun rundunar Fansan Yamma, Laftanar Kanar Abubukar Abdullahi ya bayyana cewa, a yayin farmakin an kashe ‘yan ta’adda 10 a wata arangama da suka yi a gundumar Faru da ke karamar hukumar Maradun.
Ta ce an fara kai farmakin ne a jihar Katsina, inda sojoji suka kai farmakin a kan ‘yan ta’addan a babbar filin Pauwa da ke karamar hukumar Kankara.
“Hakan ya yi sanadin kashe ‘yan ta’adda 3 tare da ceto mutane 84 da aka yi garkuwa da su.
A halin da ake ciki kuma, a jihar Zamfara, sojojin sun aiwatar da wasu ayyuka a yankin Bagabuzu da ke gundumar Faru, cikin karamar hukumar Maradun wanda ya kai ga halaka ‘yan ta’adda 7 tare da kwato babur da dai sauransu.
Bugu da kari, an yi nasarar ceto mutane 17 da wani sarkin ‘yan ta’adda ya yi garkuwa da su daga kauyukan Tsibiri da Doka da ke karamar hukumar Shinkafi, kuma a halin yanzu suna samun kulawar likitoci a wani asibiti da ke yankin.
Sanarwar ta bayyana cewa, Operation Fansan Yamma na ci gaba da jajircewa wajen tabbatar da tsaron al’ummar jihohin Katsina da Zamfara.
REL/AMINU DALHATU
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Fansar Yamma Zamfara karamar hukumar yan ta adda
এছাড়াও পড়ুন:
Hafsan sojin sama ya umarci a yawaita yi wa ’yan ta’adda ruwan bama-bamai
Hafsan Sojin Sama na Najeriya, Air Marshal Sunday Aneke, ya umarci dukkanin kwamandojin rundunar da su ƙara ƙaimi wajen yi wa ’yan ta’adda ɓarin wuta ta sama
A yayin wani taron da suka gudanar da Abuja a ranar Laraba, Aneke, ya umarci kwamandojin da su kai hare-hare masu yawa domin kare rayuka da dukiyoyin ’yan ƙasa.
Za a gudanar da wasannin ƙwallon yashi a Abuja An amince da hukuncin yi wa malamai ɗaurin shekara 14 kan lalata da ɗalibaiYa ce, “Dole ne yayin kowane aiki a nuna ƙwarewa da ƙaunar ƙasa.”
Mai magana da yawun rundunar, Air Commodore Ehimen Ejodame, ya ce taron ya mayar da hankali kan duba dabarun aiki da kuma ƙarfafa haɗin kai a tsakanin kwamandoji.
Ya ce, “Taron ya samar da dama don daidaita dabaru da tabbatar da cewa rundunar sojin sama tana ci gaba da zama ginshiƙi wajen tsaron ƙasa.”
Aneke, ya kuma jaddada muhimmancin haɗin kai a tsakanin sojin sama, sojin ƙasa, sojin ruwa da sauran hukumomin tsaro domin samun nasara tare.
Ya ce dole ne hare-haren su kasance bisa bayanan sirri da kuma tsari mai kyau don cimma sakamako mai ɗorewa.
Shugaban sojin sama ya tabbatar da cewa za su inganta walwalar jami’ai tare da ba su ƙarin horo da kayan aiki na zamani domin ƙara musu ƙwarewa a fagen fama.
Haka kuma ya yi alƙawarin bai wa ƙirƙire-ƙirƙire da fasaha muhimmanci a cikin ayyukan rundunar.
Hakazalika, Aneke ya tabbatar da cewa rundunar sojin saman za ta ci gaba da mara wa Gwamnatin Tarayya baya wajen tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali.
Ya ce rundunar za ta ci gaba da yin aiki cikin ladabi, mutunci da ƙwarewa.