Sabon Kwamishinan ‘Yan Sandan Kano Yayi Alkawarin Inganta Tsaro
Published: 20th, March 2025 GMT
Sabon kwamishinan ‘yan sandan jihar Kano, CP Ibrahim Bakori, ya sha alwashin yin aiki da gaskiya domin inganta tsaron rayuka da dukiyoyi.
CP Bakori ya bayyana hakan ne a lokacin da yake zantawa da manema labarai a hedikwatar hukumar dake Bompai Kano.
CP Bakori, wanda kwanan nan ya karbi mukamin kwamishinan ‘yan sanda na 47 a jihar, ya ce daga cikin abubuwan da ya sa a gaba sun hada da magance ‘yan daba da kuma laifuka.
CP Bakori ya bayyana matsalar ‘yan daba, fadan daban, satar wayar hannu, da shaye-shayen miyagun kwayoyi a tsakanin matasa.
Sabon Kwamishinan ya jaddada muhimmancin aikin ‘yan sandan al’umma, da nufin karfafa alaka tsakanin jami’an tsaro da jama’a.
Nadin na CP Bakori ya biyo bayan karin girma da aka yi wa magabacinsa zuwa mukamin mataimakin sufeto-Janar na ‘yan sanda (AIG). Da dimbin gogewarsa da jajircewarsa wajen inganta tsaro, mazauna Kano za su iya sa ran samun yanayi mai aminci da tsaro a karkashin jagorancinsa.
ABDULLAHI JALALUDDEEN KANO
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Tsaro
এছাড়াও পড়ুন:
An kama mutum 3 kan zargin safarar yara 17 a Zariya
Rundunar ’yan sandan Jihar Kaduna ta cafke wasu mutum uku da ake zargi da safarar bilAdama wadanda aka ceto yara 17 daga hannunsu a garin Zariya.
Wata sanarwa da Jami’in Hulɗa da Jama’a na rundunar, DSP Mansir Hassan, ya fitar, ta bayyana cewa yaran da aka ceto ana zargin an shirya safarar su ne zuwa Abuja da wasu sassan ƙasar da ma ƙetare.
An dakatar da Hakimi da Dagaci kan rikicin manoma da makiyaya a Gombe Atiku ya karyata ba sojan da ya yi takaddama da Wike kyautar motar SUVSanarwar ta bayyana cewa “an tari hanzarin ababen zargin ne da misalin ƙarfe huɗu na yammacin ranar 12 ga watan Nuwamba.
“A wannan lokaci ne jami’an sashen Ɗan Magaji da ke Zariya suka kai samame bayan samun rahoton cewa wasu mutane na shirin safarar yara da ke tafe a ƙarƙashin gadar Ɗan Magaji da ke unguwar Wusasa.
Ya bayyana cewa “waɗanda ake zargin sun haɗa da Musa Shu’aibu, mai shekara 21 daga Funtua, Jihar Katsina; Sani Mamman, mai shekara 23 daga Ingawa, Jihar Katsina; da Mubarak Ismail, mai shekara 20 daga Unguwa Uku ta Jihar Kano.
Kakakin ya ce, yayin bincike waɗanda ake zargin sun amsa cewa su ne suka tattaro yaran daga wurare daban-daban da zummar kai su Abuja kafin jami’an ’yan sanda su damƙe su.
DSP Hassan ya ƙara da cewa, yaran duk ƙanana ne, kuma suna cikin ƙoshin lafiya da yanzu haka suna hannun rundunar, yayin da ake ci gaba da ƙoƙarin gano iyayensu ko masu kula da su.
Kwamishinan ’yan sanda na Jihar Kaduna, CP Rabiu Muhammad, ya yaba da bajintar jami’an sashen Dan Magaji, inda ya nanata cewa rundunar ba za ta lamunci duk wani nau’in safarar yara ko cin zarafin su ba.
Ya kuma shawarci iyaye da masu kula da yara da su ci gaba da lura da lafiyar da walwalar ’ya’yansu, tare da faɗakar da su kan haɗarin safarar yara.