An bukaci masu hannu da shuni da ‘yan kasuwa da ma daidaikun jama’a su rika tallafawa mata da matasa da dukkanin abin da Allah ya hore mu domin ganin sun iya dogara da kansu.

Kogunan Kasar Hausa Alhaji Aliyu Da’u Abubakar ne yayi wannan kiran a wajen bada tallafi ga mata da matasa fiye da dari hudu da Kungiyar Matasan Abban Gandun Albasa Kano ta shirya a Kano.

Kogunan Kasar Hausa ya bayyana cewa irin wannan tallafi zai taimaka matukar gaske wajen karfafa mata da matasa su tsaye da kafafun su.

Yayi bayanin cewa babu shakka wadannan matasan zasu dogara da kansu kana da daukar dawainiyar iyalansu da wannan tallafi.

Taron da aka gudanar a asabar ta karshen mako ya shedi yadda mata da matasa suka sami tallafi kudi daga Naira dubu goma zuwa ashirin dai dai da yadda Allah ya tsaga da rabon mutum.

Wannan tallafin da aka ba masu kananan sana’o’i zai taimaka matukar gaske a cewa Uban Taron kuma Kogunan Kasar Hausa Alhaji Aliyu Da’u Abubakar lokacin da yake magana da Radiyo Nijeriya Kaduna.

Daga cikin wadanda suka amfani da wannan tallafin wacce tayi magana a madadin dukkanin wadanda suka amfana Zainab Adamu tayi godiya ga Kungiyar Matasan Matasan Abban Gandun Albashi da wannan jinkai da ya musu.
Cov/Zainab Adamu

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: wannan tallafi

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

Bug da kari Tinubu ya jinjina wa Shugaban jami’ar, Farfesa Wahab Olasupo Egbewole (SAN)da ‘yan tawagarsa wajen maida hankalin da suka yi na bunkasa Jami’ar da kumna kudurinta na muradun ci gaban da ake bukata.

Shi ma anashi jawabin Shugaban Jami’ar Sarkin Katsina, Alhaji. Abdulmumin Kabir Usman, wanda Wazirin Katsina, Sanata Ibrahim Idah ya wakilta, ya nuna jin dadinsa kan irin kokarin da UNILORIN saboda bunkasar ilimi da kumasamar wuraren koyon kaaratu masu kyau da kuma suka dace.

Ya yi ma kallon ayyukan da ak kaddamar a matsayin“ irin abubuwan da ake bukatar gani ke nan”da za su taimakawa lamarin koyarwa, koyo,da kuma bincike, inda ya kara da cewa yadda Jami’ar ta maida hankalinta wajen bunkasa dabarar koyon yin abubuwa zai taimakawa dalibai su tashi da sun koyi abubuwan da zasu yi baya rayuwar da suka yi cikin aji.

A nashi jawabin mataimakin Shugaban Jami’ar, Farfesa. Egbewole ya nuna farin cikinsa da godew a Shugaban kasa Tinubu kan yadda ya amince da gaiyar da Jami’ar ta yi ma shi, da kuma taimaka mata wajen tafiyar da bunkasar abubuwan jin dadi.

“Muna nan muna sa ido saboda ci gaban samun abubwan da suke taimakawa ci gaba kwarai da gaske a kowace rana kamar yadda yace yana da amincewa da yardarm ci gaba da samun hakan’’.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna November 1, 2025 Manyan Labarai Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami November 1, 2025 Manyan Labarai Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 20, Sun Ceto Mutane 17 Da Aka Yi Garkuwa Da Su November 1, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • 2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su
  • Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?
  • An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano
  • Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori
  • Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar
  • Gwamnatin Jihar Kwara Ta Kafa Kwamitoci 2 Don Tantance Wadanda Suka Yi Ritaya
  • Manoma a Jigawa Sun Jinjinwa Kungiyar Sasakawa Africa Bisa Bada Tallafi a Harkar Noma
  • Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar
  • Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Daliban Makarantar Kudi Suka Fi Na Gwamnati Kokari