Gwamnatin Kasar Iran Ta Yi Allawadai Da Hare-Haren HKI Kan Kasar Yemen
Published: 8th, July 2025 GMT
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Isma’el Baka’e ya yi allawadai da hare-haren da jiragen yakin HKI suka kai kan wasu yankuna a kasar Yemen a ranar Lahadi.
Kamfanin dillancin labaran Tasnim na kasar Iran ya nakalto Baghaee yana fadar haka a jiya litinin ya kuma yi tir da hare-hare kan a Hudaydah, Ras-Isa, as-Salif da kuma tashar wutan lantarki na Ras al-Kathib.
Har’ila yau Baka’ee ya yi allawadai da kai hare-hare kan cibiyar tattalin arziki na kasar ta Yemen a Hudaida, wadanda suka hada da kayakin jama’a wadanda suka hada da gadoji da hanyoyiu da tashar Jiragen sama, da tashar jiragen ruwa da kuma rumbunan ajiyar abinci. Wandanda gaba dayansu yin hakan ya sabawa dokokin kasa da kasa.
Hare-harin ranar Lahadi dai sune na farko bayan kimani wata guda, sannan sun zo ne bayan da yahudawan suke ce wai sun kakkabo dukkan makamai masu linzami wadanda sojojin kasar Yemen suke kaiwa kan HKI.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Al’ummar A sassan Duniya Sun Gudanar Da Zanga-Zangar Goyon Bayan Falasdinawa
An sake gudanar da wani sabuwar zanga-zanga a manyan biranen duniya domin neman kawo karshen kisan kiyashin da ake yi a Gaza
A jiya asabar ne aka sake gudanar da wata sabuwar zanga-zanga a kasashe da dama na duniya domin nuna adawa da hare-haren da gwamnatin ‘yan sahayoniyya ke ci gaba da kai wa kan zirin Gaza, wanda ya yi sanadin mutuwar Falasdinawa sama da 192,000 tare da jikkata yawancinsu mata da kananan yara.
A cewar cibiyar yada labaran Falasdinu, mutane da dama ne suka gudanar da zanga-zanga a gaban ma’aikatar harkokin wajen kasar a Quito babban birnin kasar, domin nuna goyon bayansu ga Falasdinawa a zirin Gaza.
Masu zanga-zangar sun yi kira da a kawo karshen yaki da kisan kare dangi a Gaza. Sun daga tutocin Falasdinawa da tutocin nuna kyamar yaki, yayin da wasu ke dauke da jajayen fulawa da aka lullube da fararen fulawa, wanda ke nuna alamar girmamawa ga yaran Gaza da aka kashe.
A Faransa, masu zanga-zangar sun yi maci a kan titunan birnin Paris, suna neman kawo karshen kisan kiyashin da gwamnatin mamayar Isra’ila ke ci gaba da yi kan al’ummar Falasdinu.
Masu zanga-zangar sun yi Allah wadai da rashin mutunta dokokin kasa da kasa tare da yin kira ga kasashen yamma karkashin jagorancin Faransa da su kakaba wa gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila takunkumi mai tsanani.