HausaTv:
2025-07-08@10:34:28 GMT

HKI Tana Tana Son Ci Gaba Da Yaki Kuma Trump Yana Tare Da Shi

Published: 8th, July 2025 GMT

Wata majiya wacce bata son a bayyana sunanta a nan Iran ta fadawa tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran kan cewa a ziyarar da Benyamin Natanyaho yake yi a halin yanzu a kasar Amurka ya nuna cewa yana son ci gaba da yaki da kasar Iran sannan da alamun shugaba Trump yana tare da shi.

Labarin ya kara da cewa matsayin shuwagabannin biyu a yanzun bai da bambanci da matsayinsu bayan yakin kwanaki 12.

Majiyar ta bayyaa cewa Iran a shirye take ta kare kansa, kuma tana ganin ziyarar da Natanyahu yake a Amurka duk yaudara ce, saboda tuni sun rika sun yanke shawara kan ci gaba da yaki.

Dangane da sake dawowa kan teburin tattaunawa da Amurka kuma, majiyar ta ce, Idan Trump yana ganin da sauki zamu sake komawa kan teburin tattauna da shi, yana ruda kansa ne.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Olubadan Na Ibadan Ya Rasu Yana Da Shekara 90

Olubadan na Ibadan, Oba Owolabi Olakulehin ya rasu, yana da shekara 90 a duniya.

Kakakin iyalan basaraken ne ya tabbatar da mutuwarsa da safiyar yau Litinin cikin wani saƙo da ya aike wa manema labarai.

Kwanaki biyu da suka gabata ne basaraken ya gudanar da bikin cikarsa shekara 90 a duniya a wani ƙasaitaccen biki da aka gudanar a fadarsa.

A shekarar da ta gabata ne aka naɗa Sarki Olakulehin a matsayin Olubadan na Ibadan bayan rasuwar wanda ya gabace shi Sarki Alli Okunmade II.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasar China Ta Yi Watsi da Barazanar Trump Na Kakabawa Kasashen BRICS Karin Takunkuman Tattalin Arziki
  • Reuters: Amurka Tana Da Shirin Korar Falasdinawa Daga Gaza
  • Firaministan Kasar Sin: Kasarsa Ta Kimtsa Tsaf Wajen Inganta Aikin BRI Da Bunkasa Kasuwanci Da Zuba Jari Tare Da Habasha
  • Bidiyon tsiraici: Babiana ta sake jawo ce-ce-ku-ce
  • Olubadan Na Ibadan Ya Rasu Yana Da Shekara 90
  • Olubabadan ya rasu yana da shekara 90
  • An kama ɗan Najeriya yana taimaka wa Rasha a yaƙinta da Ukraine
  • Imam Khaminae Ya Halarci Makokin Ashoora A Gidansa A Tehran
  • Shugaban Kasar Iran Ya Ce Kungiyar ECO Ta Yi Tir Da Hare-Haren HKI Kan Kasarsa