Leadership News Hausa:
2025-07-08@11:12:29 GMT

ASUU Ta Tsunduma Yajin Aiki A Faɗin Nijeriya

Published: 8th, July 2025 GMT

ASUU Ta Tsunduma Yajin Aiki A Faɗin Nijeriya

“Wannan yajin aiki ba wata sabuwar tattaunawa ba ce,” in ji shi.

“Abin da muke yi kawai martani ne ga halin ƙunci da mambobinmu ke ciki. Ofishin Akanta-Janar na ƙasa ne ke jinkirta biyan albashin da gangan.”

ASUU ta ce ta riga ta gana da hukumomin gwamnati don bayyana matsalolinta, amma ba a ɗauki mataki ba.

Farfesa Piwuna, ya kuma ƙara da cewa har yanzu malaman jami’a na bin gwamnati Naira biliyan 10 daga cikin Naira biliyan 50 da za a biya su a matsayin haƙƙoƙinsu (Earned Academic Allowances – EAA).

Ya gargaɗi gwamnati cewa duk wata jami’a da ba a biya malamanta albashi ba, za ta ci gaba da yajin aiki har sai an warware matsalar.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Gwamnatin Tarayya Yajin Aiki

এছাড়াও পড়ুন:

Gonakin Koko: Mata sun yi barazanar zanga-zanga tsirara a Kuros Riba

Wasu ƙungiyoyin mata a ƙauyukan Bendeghe-Ekiem da Abiya da ke Ƙaramar Hukumar Etung, a Jihar Kuros Riba, sun yi  barazanar gudanar da zanga-zangar tsirara idan gwamnati ba ta janye ƙudirin sayar da gonakin koko ba.

Matan sun ce wannan shawara da gwamnati ta ɗauka ba su aminta da ita ba, domin gonakin koko su ne tushen rayuwarsu, wanda da su suke cin abinci, suke biya wa ’ya’yansu kuɗin makaranta.

Kwankwaso ba zai yi mana takara a 2027 ba — NNPP Mutanen unguwa sun kama masu ƙwacen waya a Kano

Aminiya ta samu rahoton cewa gwamnati na shirin sayar da hannun jarinta a wasu manyan gonakin koko da ke wannan yanki, wanda hakan ya fusata matan da sauran al’ummar ƙauyukan da abin ya shafa.

Majiyarmu ta ce, “Idan gwamnati ta sayar da hannun jarinta, to tamkar hana mu cin moriyar aikin gonarmu ne. Wannan mataki ya saɓa wa yarjejeniyar da aka taɓa yi a baya.”

A ƙarshen mako, wasu daga cikin matan sun gudanar da zanga-zanga r lumana don nuna rashin amincewarsu da wannan ƙudiri.

Sai dai duk da ƙoƙarin sasanci daga Ma’aikatar Ayyukan Gona ta jihar, matan sun bai wa gwamnati wa’adin mako biyu ta janye shirin, ko kuma su fito su yi zanga-zangar tsirara.

Shugabannin ƙungiyoyin matan; Ntunkai Mary Obi da Cif Helen Ogar, sun roƙi Kwamishinan Ayyukan Gona, Johnson Ebokpo, da ya kai wa gwamnan kokensu, domin a samu mafita kan lamarin.

“Mun bai wa gwamnati mako biyu ta janye wannan ƙudiri ko kuma a zauna da shugabanninmu domin a cimma matsaya.”

Baya ga matan, wasu shugabannin matasa da dattawan yankin irin su Kwamared Tandu Kingsley da Mista Etta Atu-Ojua, sun goya matan baya.

Sun ce: “Idan gwamnati ta sayar da gonakin, matasa ba za su ƙara samun abin yi ba, kuma hakan zai jefa wasu cikin ayyukan daba da sata.”

Sun buƙaci gwamnatin ta sake nazari da idon basira, domin kada al’umma su shiga cikin ƙalubalen rayuwa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ASUU Ta Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Biya Albashin Watan Yuni
  • ‘Yansanda Sun Kuɓutar Da ‘Yan Ghana 19 Da Aka Yaudare Su Zuwa Nijeriya
  • Nijeriya Ba Ta Da Sha’awar Yin Gwajin Makamin Nukiliya — Shettima
  • NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19
  • Lauyoyin Majalisar Dattawan Nijeriya Sun Ƙaryata Natasha Kan Cewa Kotu Ta Ce Ta Koma Bakin Aiki
  • AI Zai Maye Gurbin Ayyuka Miliyan 92 A Duniya – Farfesa Pate
  • Bincike ya nuna ’yan Najeriya ba su gamsu da gwamnatin Tinubu ba
  • Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC
  • Gonakin Koko: Mata sun yi barazanar zanga-zanga tsirara a Kuros Riba