Leadership News Hausa:
2025-12-08@12:02:26 GMT

ASUU Ta Tsunduma Yajin Aiki A Faɗin Nijeriya

Published: 8th, July 2025 GMT

ASUU Ta Tsunduma Yajin Aiki A Faɗin Nijeriya

“Wannan yajin aiki ba wata sabuwar tattaunawa ba ce,” in ji shi.

“Abin da muke yi kawai martani ne ga halin ƙunci da mambobinmu ke ciki. Ofishin Akanta-Janar na ƙasa ne ke jinkirta biyan albashin da gangan.”

ASUU ta ce ta riga ta gana da hukumomin gwamnati don bayyana matsalolinta, amma ba a ɗauki mataki ba.

Farfesa Piwuna, ya kuma ƙara da cewa har yanzu malaman jami’a na bin gwamnati Naira biliyan 10 daga cikin Naira biliyan 50 da za a biya su a matsayin haƙƙoƙinsu (Earned Academic Allowances – EAA).

Ya gargaɗi gwamnati cewa duk wata jami’a da ba a biya malamanta albashi ba, za ta ci gaba da yajin aiki har sai an warware matsalar.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Gwamnatin Tarayya Yajin Aiki

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan sanda sun kama tsohon shugaban PCACC, Muhuyi Rimin Gado a Kano

’Yan sanda sun kama tsohon Shugaban Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa ta Jihar Kano (PCACC), Muhuyi Magaji Rimin Gado.

Rahotanni sun nuna cewar wasu ’yan sanda ɗauke makamai ne suka kama shi a ofishinsa da ke Kano, bayan tafka jayayya a ranar Juma’a.

Cikakken jadawalin rukunin Gasar Kofin Duniya ta 2026 Na kashe N100bn a kan harkar tsaro a 2025 — Zulum

Waɗanda lamarin ya faru a kan idonsu, sun  ce manyan motocin ’yan sanda cike da jami’an da ke ɗauke da makamai ne suka dira ofishinsa da ke kan titin zuwa Zariya.

Sun gargaɗi mutane da kada kowa ya kusanci ofishin, inda suka yi barazanar buɗe wa duk wanda ya yi yunƙurin tsoma baki a lamarin wuta.

Muhuyi, ya nemi jami’an su nuna masa takardar kama shi ko su bayyana dalilin kama shi.

Sai dai jami’an sun ƙi bayyana komai, face cewar umarni aka ba su daga Hedikwatar ’Yan Sanda ta Ƙasa da ke Abuja.

Lauya Ridwan Zakariyya, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin, ya ce bayan tafka jayayya, daga bisani an kai Muhuyi hedikwatar ’yan sanda ta Kano da ke Bompai.

Ya ce jami’an sun ce su wani rukuni ne na musamman na Sufeto Janar na ’Yan Sanda da aka aiko daga Abuja.

Zakariyya, ya ƙara da cewa jami’an sun yi yunƙurin ƙwace wayar Muhuyi tare da yin barazanar harbi.

Wannan shi ne karo na biyu da ake kama Muhuyi a shekarar 2025.

A farkon watan Janairu, rundunar IGP Monitoring Unit ta kama shi kan almundahanar wasu kuɗaɗe da ake zargin suna da alaƙa da wani jigo na jam’iyyar APC, amma daga baya aka sake shi.

Ƙoƙarin jin ta bakin kakakin rundunar ’yan sandan Kano, CSP Abdullahi Kiyawa, ya ci tura, domin bai amsa wayarsa ba, zuwa lokacin haɗa wannan rahoto.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tawagar Majalisar Amurka ta iso Nijeriya Don Bincika Zargin Tauye Haƙƙin Addini
  • Sojoji sun yi juyin mulki a Jamhuriyar Benin
  • Ma’aikatar Ayyuka da Sufuri ta Jigawa Ta Bada Kiyasin Kasafin Kudi na Sama da Naira Biliyan 161
  • ’Yan bindiga sun harbe ɗan sanda har lahira a Edo
  • Ranar Sabuwar Shekara za mu rufe duk na’urar POS mara rajista —Gwamnati
  • Mutum 3 sun mutum yayin haƙar rijiya a Kano
  • Sabuwar Dokar CBN: Nawa Za a Iya Cirewa a ATM da POS?
  • Shugaban Majalisar Dattawan Akpabio ya Nemi Sanata Natasha ta Biya Shi Diyyar Biliyan 200
  • Amurka ta Faɗaɗa Jerin ƙasashen Afrika Da ta Sanya wa Takunkumin Visa
  • ’Yan sanda sun kama tsohon shugaban PCACC, Muhuyi Rimin Gado a Kano