’Yan bindiga sun sace shugaban kasuwar kayan miya ta Akinyele a Oyo
Published: 20th, March 2025 GMT
Wasu ’yan bindiga sun kai hari Kasuwar Kayan Miya ta Akinyele, kusa da Ibadan, Babban Birnin Jihar Oyo, inda suka sace Shugaban Kasuwar, Alhaji Usman Yako.
Bayanan da muka samu daga shugabannin kasuwar sun nuna cewa lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 7 na dare, jim kadan bayan an idar da sallar Magriba.
Mataimakin Shugaban Kasuwar, Alhaji Abdul’aziz Abdulwasi’u (Dan Kashi), ya tabbatar da faruwar lamarin.
“Bayan na koma gida domin shan ruwa, sai yarona ya kira ni ta waya ya shaida min cewa wasu mutane ɗauke da bindigogi sun shigo kasuwa suna harbe-harbe.
“Sun tilasta Shugaban Kasuwa Alhaji Usman Yako ya fito daga motarsa suka kuma tafi da shi a cikin motarsu.”
Shi ma wani ɗan kwamitin kasuwar, Alhaji Abubakar Garba Karaye, ya ce: “Bayan mun idar da sallar Magriba a babban masallacin kasuwa, sai muka ji ƙarar harbe-harbe.
“Lokacin da muka leƙa, sai muka ga wasu mutane suna harbi a kusa da motar Shugaban Kasuwa.
“Bayan sun gama, suka ɗauke shi suka tafi da shi a cikin motarsu, sun bar tasa motar a kasuwa da harbin bindiga a jikinta.”
Shugabannin kasuwar sun ce ba a taɓa samun irin wannan hari tun bayan kafuwar kasuwar shekaru huɗu da suka gabata ba.
Sai dai kafin wanzuwar kasuwar, an yi ta samun rahoton wasu mutane da ake zargi suna ɓoyewa a cikin dazukan da ke kewayen kasuwar.
Har yanzu ba a samu jin ta bakin Kakakin Rundunar ’Yan Sandan Jihar Oyo ba, domin ba ya ɗaukar waya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Alhaji Usman Yako Kasuwar Akinyele Kasuwar Kayan Miya Shugaban Kasuwa
এছাড়াও পড়ুন:
Peter Obi ya kai wa Obasanjo ziyara
Ɗan takarar jam’iyyar Labour a zaɓen shugaban ƙasa na 2023, Peter Obi, ya ziyarci tsohon shugaban ƙasa, Olusegun Obasanjo, da kuma sabon Olubadan na Ibadan, Rashidi Ladoja, a wani zagayen ganawa da manyan ’yan siyasa gabanin zaɓen 2027.
Obi, wanda ke ƙoƙarin ƙara yauƙaƙa zumunci da manyan shugabanni a fadin ƙasar, ya bayyana cewa ziyarar na da alaƙa da burinsa na ganin an samu shugabanci na gaskiya da riƙon amana a Najeriya.
An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar KEDCO ya ƙaryata asibitin AKTH kan mutuwar majinyata saboda ɗauke wutaA wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X, Obi ya bayyana cewa ziyararsa ta musamman zuwa Ibadan na da nufin girmama Rashidi Ladoja, wanda aka naɗa a matsayin Olubadan, da kuma jaddada muhimmancin Ibadan a siyasa, zamantakewa, da tattalin arzikin ƙasar.
“Na kai ziyara don girmama sabon Olubadan, Rashidi Ladoja, wanda ƙwarewarsa a matsayin tsohon sanata, gwamna, kuma attajiri za ta taimaka wajen ɗaga martabar Ibadan,” in ji Obi.
Ya ƙara da cewa tattaunawarsa da Obasanjo da Ladoja na da nasaba da ci gaban Najeriya da kuma shugabanci da ke da burin sauya al’umma ta fuskar gaskiya da adalci.
Ziyarar Obi na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da shirye-shiryen siyasa gabanin babban zaɓen shekarar 2027, inda ake hasashen zai sake tsayawa takarar shugaban ƙasa.