Aminiya:
2025-09-17@22:10:43 GMT

’Yan bindiga sun sace shugaban kasuwar kayan miya ta Akinyele a Oyo

Published: 20th, March 2025 GMT

Wasu ’yan bindiga sun kai hari Kasuwar Kayan Miya ta Akinyele, kusa da Ibadan, Babban Birnin Jihar Oyo, inda suka sace Shugaban Kasuwar, Alhaji Usman Yako.

Bayanan da muka samu daga shugabannin kasuwar sun nuna cewa lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 7 na dare, jim kadan bayan an idar da sallar Magriba.

Ƙungiyoyin ƙwadago sun buƙaci Tinubu ya mayar da Fubara kan kujerarsa Goman Ƙarshe: Dama ta ƙarshe ga mai neman rahamar Allah

Mataimakin Shugaban Kasuwar, Alhaji Abdul’aziz Abdulwasi’u (Dan Kashi), ya tabbatar da faruwar lamarin.

“Bayan na koma gida domin shan ruwa, sai yarona ya kira ni ta waya ya shaida min cewa wasu mutane ɗauke da bindigogi sun shigo kasuwa suna harbe-harbe.

“Sun tilasta Shugaban Kasuwa Alhaji Usman Yako ya fito daga motarsa suka kuma tafi da shi a cikin motarsu.”

Shi ma wani ɗan kwamitin kasuwar, Alhaji Abubakar Garba Karaye, ya ce: “Bayan mun idar da sallar Magriba a babban masallacin kasuwa, sai muka ji ƙarar harbe-harbe.

“Lokacin da muka leƙa, sai muka ga wasu mutane suna harbi a kusa da motar Shugaban Kasuwa.

“Bayan sun gama, suka ɗauke shi suka tafi da shi a cikin motarsu, sun bar tasa motar a kasuwa da harbin bindiga a jikinta.”

Shugabannin kasuwar sun ce ba a taɓa samun irin wannan hari tun bayan kafuwar kasuwar shekaru huɗu da suka gabata ba.

Sai dai kafin wanzuwar kasuwar, an yi ta samun rahoton wasu mutane da ake zargi suna ɓoyewa a cikin dazukan da ke kewayen kasuwar.

Har yanzu ba a samu jin ta bakin Kakakin Rundunar ’Yan Sandan Jihar Oyo ba, domin ba ya ɗaukar waya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Alhaji Usman Yako Kasuwar Akinyele Kasuwar Kayan Miya Shugaban Kasuwa

এছাড়াও পড়ুন:

Peter Obi ya kai wa Obasanjo ziyara

Ɗan takarar jam’iyyar Labour a zaɓen shugaban ƙasa na 2023, Peter Obi, ya ziyarci tsohon shugaban ƙasa, Olusegun Obasanjo, da kuma sabon Olubadan na Ibadan, Rashidi Ladoja, a wani zagayen ganawa da manyan ’yan siyasa gabanin zaɓen 2027.

Obi, wanda ke ƙoƙarin ƙara yauƙaƙa zumunci da manyan shugabanni a fadin ƙasar, ya bayyana cewa ziyarar na da alaƙa da burinsa na ganin an samu shugabanci na gaskiya da riƙon amana a Najeriya.

An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar KEDCO ya ƙaryata asibitin AKTH kan mutuwar majinyata saboda ɗauke wuta

A wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X, Obi ya bayyana cewa ziyararsa ta musamman zuwa Ibadan na da nufin girmama Rashidi Ladoja, wanda aka naɗa a matsayin Olubadan, da kuma jaddada muhimmancin Ibadan a siyasa, zamantakewa, da tattalin arzikin ƙasar.

“Na kai ziyara don girmama sabon Olubadan, Rashidi Ladoja, wanda ƙwarewarsa a matsayin tsohon sanata, gwamna, kuma attajiri za ta taimaka wajen ɗaga martabar Ibadan,” in ji Obi.

Ya ƙara da cewa tattaunawarsa da Obasanjo da Ladoja na da nasaba da ci gaban Najeriya da kuma shugabanci da ke da burin sauya al’umma ta fuskar gaskiya da adalci.

Ziyarar Obi na zuwa ne a daidai lokacin da ake ci gaba da shirye-shiryen siyasa gabanin babban zaɓen shekarar 2027, inda ake hasashen zai sake tsayawa takarar shugaban ƙasa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Karamar Hukumar Birnin Kano Ta Kaddamar Da Kula Da Lafiyar Ido Kyauta
  • Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu
  • Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno
  • Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
  • ’Yan bindiga sun sace mutum 40 a masallaci a Zamfara
  • An Karrama Farfesa Adamu Gwarzo Kan Gudummawarsa Ga Bunƙasa Ilimin Jami’a A Nijeriya
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara
  • Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Shan Ƙasa, Sun Yi Garkuwa Da Masallata A Zamfara 
  • Peter Obi ya kai wa Obasanjo ziyara
  • Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi