Aminiya:
2025-09-18@00:43:34 GMT

Gwamnatin Tinubu na shirya mana zagon ƙasa — ADC

Published: 8th, July 2025 GMT

Jam’iyyar ADC ta zargin Fadar Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinuba da shirya mana wata kutungwila mai hadarin gaske domin kawo cikas ga  hadakar ’yan adawan da ke kara samun farin jini.

Sakataren Yada Labarai na ADC na Kasa, Malam Bolaji Abdullahi, ya ce a sakamakon haka gwamnatin APC a matakin kasa ta kira wani taron sirri tsakanin wasu manyan jami’an gwamnati da shugabbanin jam’iyyar ADC na jihohi da kuma kusoshinta daga yankin Arewa maso Yamma da Arewa maso Gabas.

Bolaji Abdullahi ya ce, “muna da sahihan bayanan sirri cewa manufar taron ita ce domin razanawa da tursasa wadannan shugabannin jam’iyar su shirya wa ’yan adawar makarkashiya. Wannan ba siyasa ba ce, tsurku ce.”

Ya ci gaba da cewa, hadafin taron na su shi ne “kawo rudani a jam’iyyarmu, bayyana shugabanninta a matsayin haramtattu da kum kawar da ita daga manufofin da ta sanya a gaba, lura da karuwar yadda jam’iyyar take kara samun farin jini a tsakanin ’yan Najeriya

“Wannan shirin na karkatar da hankalin ciyamomin ADC na jihohi da jami’an gwamnati da ya kamata su mayar da hankali kan warware matsalar tsaron da saurannsu da suka addabi kasa, suke yi, ba komai ba ne face hari ga tsarin dimokuradiyya.

“Daga haka ake fara samun kasa mai tsarin jam’iyya daya—ta hanyar barazaa,” in ji jami’in na ADC.

Ya ci gaba da cewa, “Hadar ADC ta rikita APC kuma yanzu ta bayyana cewa Gwamnatin Tiubu wadda ta rasu goyon  bayan ’yan Najeriya ba za ta iya jure matsin da take ciki a sakamakon wannan hadaka da nagarta ba.

“Amma kuma a maimakon ta gyara kurakurenta sai ta kare da kokarin amfani da tsohuwar dabararta ta kawo rudani a jam’iyyun adawa.”

Bolaji Abdullahi ya ce jam’iyyar ta ’yan Najeriya ce, wadanda suka gaji da karairayi da yaudara da kuncin rayuwa. Ta ’yan Najeriya ne masu burin dawo da martaba da kyakkyawan fata da kuma adalci a shugabanci. “Saboda haka ba za mu bar wasu tsirarun mutane masu kama-karya su mayar da kasar nan mai jam’iayya daya ba. Hallo kane a kan kowannenmu ya yaƙi hakan ta yadda ya kamata.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: adawa jam iyya yan Najeriya

এছাড়াও পড়ুন:

Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye

Saboda wannan baiwa daga Allah, iyalai da ‘yan uwan mai akuyar suka sanar da shirye-shiryen gudanar da bikin murnar haihuwar ‘ya’yan akuyar a ranar Lahadi mai zuwa a Garun Dakasoye, karamar hukumar Garun Malam ta Jihar Kano, inda za a yi musu suna da kuma karatun Alkur’ani mai girma.

 

A nasa bangaren, mahaifin budurwar, Malam Aliyu dake Garin Dakasoye, ya tabbatar da cewa za su gudanar da bikin domin nuna godiya ga Allah Madaukakin Sarki bisa wannan ni’ima da ya ba su.

 

Ya kara da cewa: “Mun gode wa Allah bisa wannan arziki, kuma muna sa ran gudanar da bikin tare da sanya musu suna domin nuna godiya ga Allah mai daukaka.”

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Sabon Tsarin Kula Da Lafiyar Mata Masu Juna Biyu Da Kananan Yara
  • Tinubu Ya Janye Dokar Ta-baci A Jihar Rivers
  • Al’ajabi: Yadda Aka Shirya Bikin Haihuwar ‘Ya’yan Awaki Biyar A Garin Dakasoye
  • Tinubu ya janye dokar ta-ɓaci da ya sanya a Ribas
  • Tinubu bai shirya gudanar da sahihin zaɓe ba a 2027 – Buba Galadima
  • Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu
  • ALGON ta karrama Gwamna Buni da lambar yabo kan kawo ci gaba a Yobe
  • Najeriya Na Asarar Dala Biliyan 10 Bayan Girbi Duk Shekara- Gwamnatin Tarayya
  • Gwamnatin Kano ta gayyaci Mai Dubun Isa da Shehi Tajul-Izzi kan shirya muƙabala
  • Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta