Aminiya:
2025-11-02@03:38:03 GMT

Gwamnatin Tinubu na shirya mana zagon ƙasa — ADC

Published: 8th, July 2025 GMT

Jam’iyyar ADC ta zargin Fadar Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinuba da shirya mana wata kutungwila mai hadarin gaske domin kawo cikas ga  hadakar ’yan adawan da ke kara samun farin jini.

Sakataren Yada Labarai na ADC na Kasa, Malam Bolaji Abdullahi, ya ce a sakamakon haka gwamnatin APC a matakin kasa ta kira wani taron sirri tsakanin wasu manyan jami’an gwamnati da shugabbanin jam’iyyar ADC na jihohi da kuma kusoshinta daga yankin Arewa maso Yamma da Arewa maso Gabas.

Bolaji Abdullahi ya ce, “muna da sahihan bayanan sirri cewa manufar taron ita ce domin razanawa da tursasa wadannan shugabannin jam’iyar su shirya wa ’yan adawar makarkashiya. Wannan ba siyasa ba ce, tsurku ce.”

Ya ci gaba da cewa, hadafin taron na su shi ne “kawo rudani a jam’iyyarmu, bayyana shugabanninta a matsayin haramtattu da kum kawar da ita daga manufofin da ta sanya a gaba, lura da karuwar yadda jam’iyyar take kara samun farin jini a tsakanin ’yan Najeriya

“Wannan shirin na karkatar da hankalin ciyamomin ADC na jihohi da jami’an gwamnati da ya kamata su mayar da hankali kan warware matsalar tsaron da saurannsu da suka addabi kasa, suke yi, ba komai ba ne face hari ga tsarin dimokuradiyya.

“Daga haka ake fara samun kasa mai tsarin jam’iyya daya—ta hanyar barazaa,” in ji jami’in na ADC.

Ya ci gaba da cewa, “Hadar ADC ta rikita APC kuma yanzu ta bayyana cewa Gwamnatin Tiubu wadda ta rasu goyon  bayan ’yan Najeriya ba za ta iya jure matsin da take ciki a sakamakon wannan hadaka da nagarta ba.

“Amma kuma a maimakon ta gyara kurakurenta sai ta kare da kokarin amfani da tsohuwar dabararta ta kawo rudani a jam’iyyun adawa.”

Bolaji Abdullahi ya ce jam’iyyar ta ’yan Najeriya ce, wadanda suka gaji da karairayi da yaudara da kuncin rayuwa. Ta ’yan Najeriya ne masu burin dawo da martaba da kyakkyawan fata da kuma adalci a shugabanci. “Saboda haka ba za mu bar wasu tsirarun mutane masu kama-karya su mayar da kasar nan mai jam’iayya daya ba. Hallo kane a kan kowannenmu ya yaƙi hakan ta yadda ya kamata.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: adawa jam iyya yan Najeriya

এছাড়াও পড়ুন:

Matsalar Tsaro: Ko Sabbin Shugabannin Rundunar Soji Za Su Kawo Sauyi?

Shugabannin Rundunar tsaro da Tinubu ya sallama sun hada da shugaban rundunar tsaro ta kasa Janar Christopher Musa da shugaban sojojin ruwa, Emmanuel Ikechukwu Ogalla da shugaban sojojin sama Hassan Abubakar.

Wadanda suka maye gurbin su da idanu ya koma kan hobbasar kwazon da za su nuna su ne shugaban rundunar tsaro Olufemi Oluyede, shugaban sojojin kasa Waidi Shaibu, shugaban sojojin ruwa Idi Abbas da shugaban sojojin sama S.K Aneke sai kuma shugaban rundunar leken asiri, EAP Undiendeye wanda ya ci-gaba da rike kujerar sa.

Yan Nijeriya sun jima suna kukan duk da kwarewa da gogewar jami’an sojojin Nijeriya da irin makuddan kudaden da gwamnati ke kashewa a sha’anin tsaro a kowace shekara amma matsalar kullum gaba- gaba take kara yi.

Yankuna da dama a Nijeriya musamman a Arewa- Maso- Yamma, Arewa- Maso- Gabas da Arewa ta tsakiya sun zama lahira kusa a bisa ga yadda barayin daji ke garkuwa da mutane, kone garuruwa da yi wa jama’a kisan kare dangi.

Gagarumar matsalar wadda tuni ta zama tamkar ruwan dare a tsayin shekaru ta ci dimbin rayuka da dukiyoyin al’umma ba adadi ba tare da samun gagarumar nasarar dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali a cikin al’umma ba.

Masana tsaro sun bayyana ra’ayoyi mabambanta kan sauye- sauyen. Wasu na ganin cewa sabbin jini za su iya kawo canji, yayin da wasu suka yi gargadin cewa sauya shugabanni kadai ba zai wadatar ba idan ba a yi gyaran tsari ba.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda  October 30, 2025 Manyan Labarai Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC October 30, 2025 Manyan Labarai Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai October 30, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rikicin PDP: Tsagin Wike ya dakatar da Damagum
  • Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini ba — Tinubu
  • Zargin Kisan Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini — Tinubu
  • Sanata Sunday Marshall Katung Ya Sauya Sheka Zuwa Jam’iyyar APC
  • Za mu ci gaba da shirye-shiryen babban taronmu — PDP
  • Kotu ta dakatar da gudanar da babban taron PDP
  • Kotu ta dakatar da babban taron PDP na ƙasa
  • Kotu ta dakatar da babban taron PDP
  • Matsalar Tsaro: Ko Sabbin Shugabannin Rundunar Soji Za Su Kawo Sauyi?
  • ACF ta mara wa gwamnatin Tinubu baya