HausaTv:
2025-07-08@22:47:51 GMT

 Wani Fim Din Iran Mai Ya Sami Kyauta A Baje-Kolin Fina-finai Na Shanghai

Published: 8th, July 2025 GMT

Fim din  Iran mai taken: Akharin Kuse Nahang” wanda Ramtin Balf ya shirya shi ya samu kyauta a baje kolin fina-finan ta Shangahi.

Shugaban ma’aikakar al’adu da koyarwar musulunci ta Iran a yankin Bu-Shehr Muhammad Hussain Zaduyan ya sanar da cewa; Fim din wanda na ilmantarwa ne, yana daga cikin fina-finai masu muhimmanci da aka fitar da shi a Iran.

Shi dai wannan bikin  na baje kolin fina-finai a Shanghai an yi shi ne daga ranar 3 ga watan Yuli zuwa 7 ga gare shi a wannan shekarar ta 2025.

An yi wannan bikin ne na baje-koli ne a daidai lokacin da ake yin taron kungiyar “BRICS” da taron kasashen Asiya.

Zanduyani ya kuma ce; Fim din na Iran wanda yake Magana akan matsalar da ake fuskanta ta karewar wasu daga cikin halittun ruwa, kamar kifin “Shakes” ya sami kyautar a wurin wannan taron na baje koli wanda shi ne karo na 17.”

Karamin ofishin jakadancin Iran a kasar China wanda yake kula da yada ala’adun Iran, shi ne ya wakilci wanda ya shirya fim din wajen karbar kyautar da aka ba shi.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Araqchi Ya Gana Da Babban Malamin Yahudawa Mai Adawa Da ‘Yan Sahayoniyya A Gefen Taron Kungiyar BRICS

Ministan harkokin wajen kasar Iran ya gana da babban malamin yahudawa rabbi mai adawa da ‘yan sahayoniyya a gefen taron BRICS a Brazil

Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya gana kuma ya zanta da wani babban malamin yahudawa mai adawa da ‘yan sahayoniyya a gefen taron kasashen BRICS a kasar Brazil.

Rabbi Yisrael Dovid Weiss, wanda ya je Brazil domin ganawa a gefen taron BRICS, ya gana da ministan harkokin wajen Iran, inda suka yi musayar ra’ayi da shi.

Wani abin lura shi ne cewa a baya malamin ya ziyarci ofishin jakadancin Jamhuriyar Musulunci ta Iran da ke kasar Brazil bayan bude littafin ta’aziyya ga shahidan da yahudawan sahayoniyya da suke kai wa hari a                                                                    kasar hari. A cikinsa ne ya rubuta kalamai na nuna goyon bayansa ga al’umma da gwamnatin Iran tare da jajantawa iyalan shahidan da suka rasa rayukansu sakamakon zaluncin da yahudawan sahayoniyya suka dauka kan kasar Iran.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kama ɓarayin babura a Gombe
  • Sin Na Bikin Cika Shekaru 88 Da Dukkan Al’ummar Kasar Ta Fara Yakin Kin Jinin Harin Sojojin Japan
  • Sojoji Sun Fatattaki Ƴan Bindigar Da Suka Zo Sace Wani Ɗan China
  • Araqchi Ya Gana Da Babban Malamin Yahudawa Mai Adawa Da ‘Yan Sahayoniyya A Gefen Taron Kungiyar BRICS
  • Kano ta sami rahoton cin zarafin yara 351 – NHRC
  • Sheikh Ibrahim Zakzaky Ya Taya JMI Murnar Nasara A Kan Mikiyanta
  • Elon Musk zai kafa sabuwar jam’iyyar siyasa a Amurka
  • Taron Ashura Ya Zama Lamari Mafi Girma Da Cinkoson Jama’a, Inda Masu Ziyara Daga Sassan Duniya Suka Isa Karbala
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Da Tawagarsa Sun Isa Kasar Brazil Don Halartar Taron BRICS Karo Na 17