Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Najeriya (TCN) ya bukaci hukumomin tsaro da Sarakuna da kuma kungiyoyin matasa su dauki matakan gaggawa wajen dakile gina gine-gine a karkashin manyan layukan lantarki da kuma hana lalata kayan hasken lantarki.

 

Babban Manajan TCN na Yankin Kaduna, Injiniya Nasir Mansur Fada, ne ya yi wannan kira a yayin wani taron wayar da kai da aka gudanar da masu ruwa da tsaki a hedikwatar TCN da ke Mando, Kaduna.

 

Taron ya samu halartar Sarakuna da jami’an tsaro da kungiyoyin masu zaman kansu domin bin umarnin Hukumar Kula da Wutar Lantarki ta kasa domin ci gaba da kokarin da TCN kiyi na dakile mamaye filayen layin lantarki da kare dukiyoyin kasa.

 

Injiniya Nasir Mansur Fada ya jaddada muhimmancin hadin gwiwa tsakanin al’umma da hukumomin da abin ya shafa domin samun wadataccen wutan lantarki a kasan nan.

 

Ya bayyana cewa an girka sababbin nauran bayarda wuta wato transformers a wurare daban-daban tare da ci gaba da ayyukan fadada samarda hasken wutan da kuma gyaran cibiyoyin wuta a fadin jihar Kaduna.

 

Sai dai ya kuka cewa hakka ba zata cimma ruwa ba mudin al’ummomin da ke zaune a kusa da cibiyoyin wutar suka gaza sanya ido domin kare kayyakin hasken lantarkin.

 

A cikin wata makala da aka gabatar mai taken Illar Lalata Kayan Wuta a Kasa, Manaja Mai Kula da Layyukan Wutan na Yankin Kaduna, Injiniya Simon Innocent, ya bayyana cewa ayyukan lalata kayan lantarki na haifar da matsaloli wajen samun wuta da kuma durkusar da ci gaban tattalin arzikin kasa.

 

A nasa jawabin, Mataimakin Kwamandan Hukumar Tsaro ta Civil Defence (NSCDC), Ahmed Isah Audu, ya ce sanarda da jami’an akan lokaci da bayanai akan barnar da ake kan yi na da matukar muhimmanci wajen dakile ayyukan lalata kayan wuta a ko’ina cikin duniya.

 

An kammala taron wayar da kan ne tareda tattaunawa tsakanin mahalarta taron inda suka sha alwashin tallafa wa TCN tare da hada kai domin kare kayayyakin wuta da tabbatar da tsaro da ci gaba a al’umma.

COV: Adamu Yusuf

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Babbar Illar Karkashen Kayan Wayar Wayarda

এছাড়াও পড়ুন:

Gidauniyar IRM Da KADCHMA, Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna

Da yake kaddamar da shirin, Darakta Janar na IRM, Alhaji Anas Muhammad, ya ce an kirkiro da shirin ne domin karfafa zaman lafiya da hadin kai ta hanyar tallafa wa Musulmai da Kiristoci ta bangaren samar da kiwon lafiya da bayar da tallafin kayan abinci da jari.

 

Ya ce: “Kalubalen lafiya ba sa bambance addini ko kabila, don haka bama bambantawa wajen bayar da tallafin. in sha Allah zamu ci gaba da aiwatar da irin wannan shiri a fadin jihar Kaduna baki daya.”

 

A nasa jawabin, Shugaban hukumar KADCHMA, Malam Abubakar Hassan, ya bayyana cewa wannan hadin gwiwa tana nuna muhimmancin dangantaka tsakanin gwamnati da kungiyoyi masu zaman kansu wajen cimma dorewar tsarin inshorar lafiya ga kowa.

 

Ya kara da cewa kaddamar da inshorar lafiya kyauta na shekara guda babban ci gaba ne a cikin gyaran fannin lafiya da ake gudanarwa a jihar, inda ya yaba da kokarin gidauniyar IRM wajen tallafawa rayuwar al’ummar  Kaduna – Musulmai da Kiristoci.

 

Wasu daga cikin wadanda suka amfana da shirin daga Kungiyar Kiristoci ta Nijeriya (CAN) reshen Kaduna da kuma kungiyar ci gaba ta Darikar Tijjaniyya ta jihar Kaduna sun bayyana farin ciki da godiya ga gidauniyar da kuma gwamnatin jihar, inda suka ce inshorar lafiya kyauta za ta rage musu nauyin kashe kudin magani tare da karfafa hadin kai a tsakanin al’umma da samar da zaman lafiya.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Wadi Al-Salam: Maƙabartar Musulmai Mafi Girma A Duniya November 2, 2025 Ra'ayi Riga A Kan Wa Trump Ke Son Kaddamar Da Hari a Najeriya? November 2, 2025 Labarai Maganin Nankarwa (3) November 2, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gidauniyar IRM Da KADCHMA, Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna
  • Hamas ta musanta zargin Amurka na cewa tana sace kayan agaji a Gaza
  • Iran Ta Gargadi Isra’ila Kuma Tasha Alwashin Kare Shirinta Na Nukiliya
  •  Gaza: Daga Tsagaita Wuta Zuwa Yanzu Fiye Da Mutane 200 Ne Su Ka Yi Shahada
  • Najeriya ta musanta ikirarin Trump, na cewa Kristoci na fuskantar babbar barazana a kasar
  • Dan Majalisar Jema’a/Sanga, Daniel Amos, Ya Koma Jam’iyyar APC
  • Sanata Sunday Marshall Katung Ya Sauya Sheka Zuwa Jam’iyyar APC
  • HKI Na Ci Gaba Keta Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta A Gaza Inda Take Kashe Falasdinawa
  • Kasashen Pakistan Da Afghanistan Sun Tsawaita Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta
  • Allah Ya Kai Manzon Allah (SAW) Muƙami Na Babban Yabo A Cikin Komai