TCN Ta Wayar Da Kan Al’ummomin Kaduna Kan Illar Lalata Kayan Wuta Da Gini Karkashen Babbar Wayar Wuta
Published: 8th, July 2025 GMT
Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Najeriya (TCN) ya bukaci hukumomin tsaro da Sarakuna da kuma kungiyoyin matasa su dauki matakan gaggawa wajen dakile gina gine-gine a karkashin manyan layukan lantarki da kuma hana lalata kayan hasken lantarki.
Babban Manajan TCN na Yankin Kaduna, Injiniya Nasir Mansur Fada, ne ya yi wannan kira a yayin wani taron wayar da kai da aka gudanar da masu ruwa da tsaki a hedikwatar TCN da ke Mando, Kaduna.
Taron ya samu halartar Sarakuna da jami’an tsaro da kungiyoyin masu zaman kansu domin bin umarnin Hukumar Kula da Wutar Lantarki ta kasa domin ci gaba da kokarin da TCN kiyi na dakile mamaye filayen layin lantarki da kare dukiyoyin kasa.
Injiniya Nasir Mansur Fada ya jaddada muhimmancin hadin gwiwa tsakanin al’umma da hukumomin da abin ya shafa domin samun wadataccen wutan lantarki a kasan nan.
Ya bayyana cewa an girka sababbin nauran bayarda wuta wato transformers a wurare daban-daban tare da ci gaba da ayyukan fadada samarda hasken wutan da kuma gyaran cibiyoyin wuta a fadin jihar Kaduna.
Sai dai ya kuka cewa hakka ba zata cimma ruwa ba mudin al’ummomin da ke zaune a kusa da cibiyoyin wutar suka gaza sanya ido domin kare kayyakin hasken lantarkin.
A cikin wata makala da aka gabatar mai taken Illar Lalata Kayan Wuta a Kasa, Manaja Mai Kula da Layyukan Wutan na Yankin Kaduna, Injiniya Simon Innocent, ya bayyana cewa ayyukan lalata kayan lantarki na haifar da matsaloli wajen samun wuta da kuma durkusar da ci gaban tattalin arzikin kasa.
A nasa jawabin, Mataimakin Kwamandan Hukumar Tsaro ta Civil Defence (NSCDC), Ahmed Isah Audu, ya ce sanarda da jami’an akan lokaci da bayanai akan barnar da ake kan yi na da matukar muhimmanci wajen dakile ayyukan lalata kayan wuta a ko’ina cikin duniya.
An kammala taron wayar da kan ne tareda tattaunawa tsakanin mahalarta taron inda suka sha alwashin tallafa wa TCN tare da hada kai domin kare kayayyakin wuta da tabbatar da tsaro da ci gaba a al’umma.
COV: Adamu Yusuf
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Babbar Illar Karkashen Kayan Wayar Wayarda
এছাড়াও পড়ুন:
An kama ɗaya daga cikin manyan kwamandojin IPOB
Rundunar Sojin Kasa ta Najeriya ta sanar da samun nasarar cafke Ifeanyi Eze Okorienta, wanda aka fi sani da “Gentle de Yahoo”, ɗaya daga cikin manyan kwamandojin ƙungiyar IPOB, a wani samame da ta kai a yankin kudu maso gabashin ƙasar.
Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya NAN ya ruwaito wata majiya daga hedikwatar rundunar sojin tana cewa an cafke Gentle de Yahoo ne yayin farmakin da sojojin suka kai a ranar Lahadi kan sansanonin ’yan ƙungiyar a cikin wani dajin da ke ƙaramar hukumar Okigwe a Jihar Imo.
An tattauna yadda za a inganta walwalar malamai a Gombe Tinubu ya janye dokar ta-ɓaci da ya sanya a RibasMajiyar ta ce a yayin cafke jagoran na IPOB, an kuma ƙwato makamai da dama daga hannunsa, ciki har da bindigogi kirar Turai, harsasai, kakin sojoji da na ’yan sanda.
“Cafke wannan kwamanda babban ci gaba ne wajen murƙushe ayyukan ta’addanci da ƙungiyar IPOB ke aikatawa, musamman a yankunan da suke hana zaman lafiya,” in ji majiyar.
Kungiyar IPOB, wacce ke fafutukar ballewa daga Najeriya don kafa ƙasar Biyafara, ta kasance a gaba-gaba wajen aikata hare-hare da ta da tarzoma a jihohin kudu maso gabas, musamman ta hannun sashen rundunar da suka kafa da kansu mai suna Eastern Security Network (ESN).
Ana dai zargin cewa Eze yana ɗaya daga cikin jagororin da ke tsara harin kwantan bauna, da hana zirga-zirga a wasu sassan yankin, wanda hakan ya jefa al’umma cikin fargaba da zaman ɗar-ɗar.
Wannan nasara na zuwa ne bayan makonni kaɗan da wata kotu a ƙasar Finland ta yanke wa Simon Ekpa, wani babban jigo a ƙungiyar IPOB, hukuncin ɗaurin shekaru shida a gidan yari kan laifukan da suka shafi ta’addanci da tayar da zaune tsaye.
Masu sharhi na ganin cewa cafke Gentle de Yahoo wata alama ce da ke nuna cewa ana shirin ragargaza ƙungiyar IPOB gaba ɗaya, duk da cewar har yanzu akwai sauran rina a kaba, musamman ganin cewa wasu sassan yankin na ci gaba da fuskantar matsalolin tsaro.