Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Najeriya (TCN) ya bukaci hukumomin tsaro da Sarakuna da kuma kungiyoyin matasa su dauki matakan gaggawa wajen dakile gina gine-gine a karkashin manyan layukan lantarki da kuma hana lalata kayan hasken lantarki.

 

Babban Manajan TCN na Yankin Kaduna, Injiniya Nasir Mansur Fada, ne ya yi wannan kira a yayin wani taron wayar da kai da aka gudanar da masu ruwa da tsaki a hedikwatar TCN da ke Mando, Kaduna.

 

Taron ya samu halartar Sarakuna da jami’an tsaro da kungiyoyin masu zaman kansu domin bin umarnin Hukumar Kula da Wutar Lantarki ta kasa domin ci gaba da kokarin da TCN kiyi na dakile mamaye filayen layin lantarki da kare dukiyoyin kasa.

 

Injiniya Nasir Mansur Fada ya jaddada muhimmancin hadin gwiwa tsakanin al’umma da hukumomin da abin ya shafa domin samun wadataccen wutan lantarki a kasan nan.

 

Ya bayyana cewa an girka sababbin nauran bayarda wuta wato transformers a wurare daban-daban tare da ci gaba da ayyukan fadada samarda hasken wutan da kuma gyaran cibiyoyin wuta a fadin jihar Kaduna.

 

Sai dai ya kuka cewa hakka ba zata cimma ruwa ba mudin al’ummomin da ke zaune a kusa da cibiyoyin wutar suka gaza sanya ido domin kare kayyakin hasken lantarkin.

 

A cikin wata makala da aka gabatar mai taken Illar Lalata Kayan Wuta a Kasa, Manaja Mai Kula da Layyukan Wutan na Yankin Kaduna, Injiniya Simon Innocent, ya bayyana cewa ayyukan lalata kayan lantarki na haifar da matsaloli wajen samun wuta da kuma durkusar da ci gaban tattalin arzikin kasa.

 

A nasa jawabin, Mataimakin Kwamandan Hukumar Tsaro ta Civil Defence (NSCDC), Ahmed Isah Audu, ya ce sanarda da jami’an akan lokaci da bayanai akan barnar da ake kan yi na da matukar muhimmanci wajen dakile ayyukan lalata kayan wuta a ko’ina cikin duniya.

 

An kammala taron wayar da kan ne tareda tattaunawa tsakanin mahalarta taron inda suka sha alwashin tallafa wa TCN tare da hada kai domin kare kayayyakin wuta da tabbatar da tsaro da ci gaba a al’umma.

COV: Adamu Yusuf

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Babbar Illar Karkashen Kayan Wayar Wayarda

এছাড়াও পড়ুন:

Zulum ya musanta shirin ficewa daga APC

Gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum, ya ƙaryata jita-jitar da ke yawo a kafafen sada zumunta cewa zai bar jam’iyyar APC zuwa ADC tare da wasu gwamnoni biyar.

A wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Dauda Iliya, ya fitar, Zulum ya ce wannan labari ƙarya ne, kuma wasu ne kawai ke ƙirƙirarsa domin cimma wata manufa ta ƙashin kansu.

Gwamna ya gargaɗi sarakuna kan mamaye filayen kiwo a Gombe Majalisar Dattawa ta gindaya sharaɗin dawo da Sanata Natasha

Ya ce yana nan daram a jam’iyyar APC kuma yana biyayya ga jam’iyyar a matakin jiha da ƙasa baki ɗaya.

Sanarwar ta ce, “Mun ji wani labari da ake yaɗawa cewa zan koma jam’iyyar ADC tare da wasu gwamnoni biyar.

“Wannan labari ba gaskiya ba ne. Waɗanda suka ƙirƙira shi ba sa kishin ƙasa kuma ba sa taimaka wa Jihar Borno ko Nijeriya.”

Zulum ya ƙara da cewa yana nan daram a APC, domin ya damu da ci gaban Jihar Borno.

“Ina roƙon jama’ar Borno da su yi watsi da wannan jita-jita. Mu ba mu da lokacin siyasar da ba ta da amfani. Muna da aiki a gabanmu na ci gaban jiharmu,” in ji shi.

Ya kuma roƙi kafafen yaɗa labarai da su tabbatar da sahihancin labarai kafin su yaɗa su.

Hakazalika, ya bayyana cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da aiki tuƙuru a ƙarƙashin jam’iyyar APC domin ciyar da jihar gaba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Yace Mutanen Kasarsa Suna Cikin Shiri Don Kare Kansu Da Karfi
  • Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki
  • Reuters: Amurka Tana Da Shirin Korar Falasdinawa Daga Gaza
  • An Kaddamar Da Shirin Samar Da Wutar Lantarki A Jami’ar Kashere Gombe.
  • Gwamna Yusuf Ya Kaddamar Rabon Na’urorin Rarraba Lantarki 500
  • Tinubu ya umarci sojoji su murƙushe ’yan ta’adda a faɗin Najeriya 
  • Zulum ya musanta shirin ficewa daga APC
  •  IRGC: Duk Wani Wuce Gona Da Iri Na ‘Yan Sahayoniya Zai Gaggauta Rushewarsu
  •  Na’im Kassim: Kare Kasa Ba Ya Da Bukatuwa Da Izinin Kowa