Aminiya:
2025-10-20@06:15:19 GMT

Fashewar Tanka: Asibitoci sun cika da mutane a Abuja

Published: 20th, March 2025 GMT

Asibitin Ƙasa da Asibitin Asokoro da ke Abuja sun cika maƙil da mutanen da suka jikkata sakamakon fashewar tankar gas da ta auku da daren Laraba a gadar Karu.

Lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 7:14 na dare, bayan wata babbar mota ɗauke da gas ta yi hatsari, tare da faɗawa kan wasu motoci da ke kan gadar, lamarin da ya haddasa gobara.

Sarakunan Kano su kimtsa wa hawan sallah bana — Abba Fubara ya magantu bayan ayyana dokar ta ɓaci a Ribas

Rahotanni sun nuna cewa an rasa rayuka da dama, yayin da mutane da yawa suka samu munanan raunuka.

Shugaban Sashen Ɗaukar Matakan Gaggawa na Hukumar Kula da Harkokin Gaggawa ta Ƙasa (FEMA), Mista Mark Nyam, ya bayyana cewa jami’an hukumar sun isa wajen domin ceto mutanen da abin ya shafa.

Hukumar Kashe Gobara ta Tarayya da ta Babban Birnin Tarayya, ’Yan Sanda, da Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) sun duƙufa wajen kai ɗauki.

Wasu daga cikin waɗanda suka jikkata an kai su Asibitin Fadar Shugaban Ƙasa domin samun kulawar gaggawa.

Shirin Inganta Amfani da Gas (PCNG) na Fadar Shugaban Ƙasa, ya bayyana jimaminsa game da wannan hatsari.

Ya yi alƙawarin gudanar da bincike don gano musabbabin aukuwar lamarin.

Rahotanni sun nuna cewa tankar gas ɗin ta samu matsalar birki, wanda hakan ya haddasa fashewar tankin mai.

A cikin wata sanarwa, PCNG ya buƙaci jama’a da su guji yaɗa jita-jita har sai an kammala bincike.

Hakazalika, ya jaddada aniyarsa na tabbatar da aminci wajen amfani da CNG, tare da ɗaukar matakan hana aukuwar irin wannan hatsari a nan gaba.

Jami’an agaji sun ci gaba da aikin ceto da bayar da taimako ga waɗanda lamarin ya shafa, tare da ƙoƙarin shawo kan ɓarnar da gobarar ta haifar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gobara Hatsari Karu

এছাড়াও পড়ুন:

Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103 October 18, 2025 Daga Birnin Sin Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Samarwa Yankin Taiwan Makamai October 18, 2025 Daga Birnin Sin Mataimakin Firaministan Sin Ya Zanta Da Sakataren Baitul-mali Da Wakilin Cinikayyar Amurka October 18, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mahukunta sun kai samame wani gidan shan Shisha a Kano
  • An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin
  • Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya
  • NSCDC Ta Kama Wadanda Ake Zargi Da Lalata Kadarorin Gwamnati A Kaduna
  • Hukumar Gidan Yarin Kano Ta Tabbatar Da Dauke Abduljabbar Zuwa Abuja
  • Kungiyar Hamas Ta Yi Kira Da Matsa Wa Isra’ila Lamba Da Ta Cika Sharuddan Yarjejeniyar Gaza
  • Tawagar Sin Ta Dindindin A Hukumar Fao Ta Fara Aiki
  • Dantawaye ya zama sabon kwamishinan ’yan sandan Abuja
  • Dantawaye Ya Karɓi Ragamar Aiki A Matsayin Sabon Kwamishinan Ƴansandan Abuja
  • Yadda ‘Yan Bindiga Ke Zafafa Hare-hare A Jihohin Arewa Maso Yamma