Aminiya:
2025-06-30@22:40:59 GMT

Fashewar Tanka: Asibitoci sun cika da mutane a Abuja

Published: 20th, March 2025 GMT

Asibitin Ƙasa da Asibitin Asokoro da ke Abuja sun cika maƙil da mutanen da suka jikkata sakamakon fashewar tankar gas da ta auku da daren Laraba a gadar Karu.

Lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 7:14 na dare, bayan wata babbar mota ɗauke da gas ta yi hatsari, tare da faɗawa kan wasu motoci da ke kan gadar, lamarin da ya haddasa gobara.

Sarakunan Kano su kimtsa wa hawan sallah bana — Abba Fubara ya magantu bayan ayyana dokar ta ɓaci a Ribas

Rahotanni sun nuna cewa an rasa rayuka da dama, yayin da mutane da yawa suka samu munanan raunuka.

Shugaban Sashen Ɗaukar Matakan Gaggawa na Hukumar Kula da Harkokin Gaggawa ta Ƙasa (FEMA), Mista Mark Nyam, ya bayyana cewa jami’an hukumar sun isa wajen domin ceto mutanen da abin ya shafa.

Hukumar Kashe Gobara ta Tarayya da ta Babban Birnin Tarayya, ’Yan Sanda, da Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) sun duƙufa wajen kai ɗauki.

Wasu daga cikin waɗanda suka jikkata an kai su Asibitin Fadar Shugaban Ƙasa domin samun kulawar gaggawa.

Shirin Inganta Amfani da Gas (PCNG) na Fadar Shugaban Ƙasa, ya bayyana jimaminsa game da wannan hatsari.

Ya yi alƙawarin gudanar da bincike don gano musabbabin aukuwar lamarin.

Rahotanni sun nuna cewa tankar gas ɗin ta samu matsalar birki, wanda hakan ya haddasa fashewar tankin mai.

A cikin wata sanarwa, PCNG ya buƙaci jama’a da su guji yaɗa jita-jita har sai an kammala bincike.

Hakazalika, ya jaddada aniyarsa na tabbatar da aminci wajen amfani da CNG, tare da ɗaukar matakan hana aukuwar irin wannan hatsari a nan gaba.

Jami’an agaji sun ci gaba da aikin ceto da bayar da taimako ga waɗanda lamarin ya shafa, tare da ƙoƙarin shawo kan ɓarnar da gobarar ta haifar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gobara Hatsari Karu

এছাড়াও পড়ুন:

 Titunan Birnin Tehran Sun Cika Makil Da Masu Jana’izar Shahidan Ta’addancin HKI

Kamfanin Dillancin Labarun “Mehr” ya nakalto cewa;  Tun da jijjfin safiyar yau Asabar ne tasoshin jiragen kasa da na safa-safa su ka cika makil da masu son halarta babban filin Juyi na Tehran da can ne zai zama masonin rakiyar shahidan zuwa makwancinsu na karshe.

Ana iya ganin dubun dubatar mutane da su ka fito daga kowane bangare na al’ummar Iran domin halartar jana’izar ,yara, mata, masana da kwamandojin soja,  wacce ta  fara da misalin karfe 8;00 na safiyar yau agogon Tehran.

Adadin shahidan da ake jana’izar tasu a yau, sun kai 60, za kuma a rufe su ne a makabartar “Baheshti-Zahra” wacce take kunshe da shahidan juyin juya halin musulunci.

A shirnmu na rana za a ji cikakken bayani akan yadda jana’izar ta kasance.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Kasar Iran Ya Yi Kakkausar Suka Kan Hukumar Kula Da Makamashin Nukiliya Ta IAEA
  • Shugaban kasar Iran ya soki lamirin hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya IAEA
  • Dalibai 29 Suka Rasu A Turmutsitsin Tserewa Ga Fashewar Taransifoma A Jamhuriyar Afirka Ta Tsakiya
  • Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku
  • Ƙwallon Mata: Rivers United Ta Doke Nasarawa Amazons A Wasan Ƙarshe Na Kofin Shugaban Ƙasa
  • Yadda na hannun daman ’Yar’Adua ya yi tuggun hana ni zama shugaban ƙasa — Jonathan 
  • Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025
  • Iran ta Ki Amincewa Da Ziyarar Shugaban Hukumar IAEA Zuwa Kasar
  • Iran Ta Shigar Da Korafi A Hukumar Kare Hakkin Bil’adama Ta MDD
  •  Titunan Birnin Tehran Sun Cika Makil Da Masu Jana’izar Shahidan Ta’addancin HKI