Fashewar Tanka: Asibitoci sun cika da mutane a Abuja
Published: 20th, March 2025 GMT
Asibitin Ƙasa da Asibitin Asokoro da ke Abuja sun cika maƙil da mutanen da suka jikkata sakamakon fashewar tankar gas da ta auku da daren Laraba a gadar Karu.
Lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 7:14 na dare, bayan wata babbar mota ɗauke da gas ta yi hatsari, tare da faɗawa kan wasu motoci da ke kan gadar, lamarin da ya haddasa gobara.
Rahotanni sun nuna cewa an rasa rayuka da dama, yayin da mutane da yawa suka samu munanan raunuka.
Shugaban Sashen Ɗaukar Matakan Gaggawa na Hukumar Kula da Harkokin Gaggawa ta Ƙasa (FEMA), Mista Mark Nyam, ya bayyana cewa jami’an hukumar sun isa wajen domin ceto mutanen da abin ya shafa.
Hukumar Kashe Gobara ta Tarayya da ta Babban Birnin Tarayya, ’Yan Sanda, da Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) sun duƙufa wajen kai ɗauki.
Wasu daga cikin waɗanda suka jikkata an kai su Asibitin Fadar Shugaban Ƙasa domin samun kulawar gaggawa.
Shirin Inganta Amfani da Gas (PCNG) na Fadar Shugaban Ƙasa, ya bayyana jimaminsa game da wannan hatsari.
Ya yi alƙawarin gudanar da bincike don gano musabbabin aukuwar lamarin.
Rahotanni sun nuna cewa tankar gas ɗin ta samu matsalar birki, wanda hakan ya haddasa fashewar tankin mai.
A cikin wata sanarwa, PCNG ya buƙaci jama’a da su guji yaɗa jita-jita har sai an kammala bincike.
Hakazalika, ya jaddada aniyarsa na tabbatar da aminci wajen amfani da CNG, tare da ɗaukar matakan hana aukuwar irin wannan hatsari a nan gaba.
Jami’an agaji sun ci gaba da aikin ceto da bayar da taimako ga waɗanda lamarin ya shafa, tare da ƙoƙarin shawo kan ɓarnar da gobarar ta haifar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Gobara Hatsari Karu
এছাড়াও পড়ুন:
Iyaye Sun Yi Fitowar Farin Dango Don Yi Wa “Yayansu Allurar Rigakafi a Sule-Tankarkar
Daga Usman Muhammad Zaria
Aikin rigakafin watan Disamba a karamar hukumar Sule-Tankarkar ta jihar Jigawa ya samu gagarumar nasara, yayin da iyaye suka fito kwansu da kwarkwata domin tabbatar da cewa an yi wa ’ya’yansu cikakken rigakafi.
Wasu daga cikin iyayen da suka kawo ’ya’yansu domin karbar rigakafin yau da kullum da na shan inna sun bayyana jin dadinsu kan yadda aka gudanar da aikin cikin kwanciyar hankali.
Daya daga cikinsu, Malama Ummahani Danbala, ta ce an wayar da kan jama’a sosai ta hannun mata ’yan sa-kai a unguwarsu, inda aka karfafa gwiwar iyaye mata su kawo ’ya’yansu domin karbar rigakafin yau da kullum da na shan inna.
Malam Yunusa, wani mai sa ido a karamar hukumar, ya bayyana gamsuwarsa da yadda aka gudanar da aikin rigakafin a yankin.
A cewarsa, aikin wayar da kan jama’a ya yi matukar tasiri, domin mutane na kawo ’ya’yansu da kansu ba tare da kin amincewa da rigakafin ba.
Yunusa ya bayyana cewa duk da kasancewar karamar hukumar tana kan iyaka, aikin ya gudana cikin nasara, sakamakon hadin gwiwar da aka samu daga dukkan masu ruwa da tsaki.
Ya kara da cewa ana sa ran rigakafin yara kusan 45,221, inda aka yi niyyar kai rigakafin makarantu da wuraren ibada domin gano yaran da ba a musu ba.
Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa karamar hukumar na da cibiyoyin lafiya guda 28, kuma aikin rigakafin ya gudana cikin kwanciyar hankali a al’ummomin Ablasu, Kings, Amanda, Togai, Nagwamatse da Hannun Giwa.
Ana sa ran kammala zagayen rigakafin shan inna na watan Disamba a ranar Juma’a a fadin kananan hukumomi 27 na jihar Jigawa.