Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-11-03@03:59:15 GMT

An kama mataimakin shugaban Sudan ta Kudu

Published: 27th, March 2025 GMT

An kama mataimakin shugaban Sudan ta Kudu

An kama mataimakin shugaban ƙasa na farko a Sudan ta Kudu Riek Machar a babban birnin ƙasar Juba, a yayin da ake ci gaba da samun ƙaruwar zaman tankiya tsakaninsa da Shugaba Salva Kiir.

Faɗa tsakanin dakarun da ke goya wa shugabannin biyu baya ya tsananta a yankunan Rejaf da ke kudancin Juba da Wunaliet da ke yammaci.

Rahotanni sun bayyana cewa an kama shi ne tare da uwargidansa Angekina Teny.

Ana samun fargabar cewa kama shi zai iya kawo tarnaƙi ga yarjejeniyar zaman lafiya ta ƙasar.

Kama Machar na zuwa ne bayan shafe makonni ana samun tashe tashe hankula bayan shugaba Kiir ya tsare wasu daga cikin abokan Machar a farkon watan nan.

Tawagar majalisar ɗinkin duniya da ke Sudan ta Kudu tayi gargaɗin cewa ƙasar na cikin barazanar sake faɗawa cikin yaƙi, inda ta buƙaci ɓangarorin biyu suyi aiki da yarjejeniyar zaman lafiya ta 2018.

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

 

Yayin ganawarsa da firaministan Thailand, Shugaba Xi Jinping ya ce a shirye kasarsa take ta karfafa hadin gwiwa da Thailand kan dabarun samun ci gaba, tare kuma da gabatar da gogewarta na samun ci gaba a sabon zamani, kuma ya yi kira da a gaggauta gina layin dogo tsakanin Sin da Thailand da bunkasa hadin gwiwa a bangaren cinikin amfanin gona da tattalin arziki mai kiyaye muhalli da kuma kirkire kirkiren fasaha. (Mai fassara: FMM)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC October 31, 2025 Daga Birnin Sin Sin Da Amurka Suna Taimaka Wa Juna Da Samun Wadata Tare October 31, 2025 Daga Birnin Sin Xi Jinping Ya Halarci Kwarya-Kwaryan Taron Shugabannin APEC Na 32 Tare Da Gabatar Da Jawabi October 31, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jamus ta shiga sahun ƙasashen da ke neman kawo ƙarshen yaƙin Sudan
  • Kisan Kiristoci: Za mu kai hari Najeriya — Trump
  • Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 
  • An yi garkuwa da Mataimakin Shugaban Majalisar Dokokin Kebbi
  • Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace
  • Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari
  • Ya Kamata Sin Da Amurka Su Zama Kawayen Juna Ba Abokan Gaba Ba
  • Ƴansanda Sun Kama  Wani Mai Wasa Da Bindiga AK-47 A Cikin Wani Bidiyo A Adamawa
  • An sake kama shi a cikin ’yan fashi kwana 5 da fitowa daga kurkuku
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Daliban Makarantar Kudi Suka Fi Na Gwamnati Kokari