Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-06-15@19:49:19 GMT

An kama mataimakin shugaban Sudan ta Kudu

Published: 27th, March 2025 GMT

An kama mataimakin shugaban Sudan ta Kudu

An kama mataimakin shugaban ƙasa na farko a Sudan ta Kudu Riek Machar a babban birnin ƙasar Juba, a yayin da ake ci gaba da samun ƙaruwar zaman tankiya tsakaninsa da Shugaba Salva Kiir.

Faɗa tsakanin dakarun da ke goya wa shugabannin biyu baya ya tsananta a yankunan Rejaf da ke kudancin Juba da Wunaliet da ke yammaci.

Rahotanni sun bayyana cewa an kama shi ne tare da uwargidansa Angekina Teny.

Ana samun fargabar cewa kama shi zai iya kawo tarnaƙi ga yarjejeniyar zaman lafiya ta ƙasar.

Kama Machar na zuwa ne bayan shafe makonni ana samun tashe tashe hankula bayan shugaba Kiir ya tsare wasu daga cikin abokan Machar a farkon watan nan.

Tawagar majalisar ɗinkin duniya da ke Sudan ta Kudu tayi gargaɗin cewa ƙasar na cikin barazanar sake faɗawa cikin yaƙi, inda ta buƙaci ɓangarorin biyu suyi aiki da yarjejeniyar zaman lafiya ta 2018.

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Ƴansanda Sun Fara Tsananta Ɗaukar Mataki Kan Ƴan Daba A Kano

Karfafa hulda da al’umma da shugabannin yankuna don samun shawarwari kan inganta tsaro.

Ci gaba da hada kai da sauran hukumomin tsaro da masu ruwa da tsaki don samun nasara a yaki da daba.

Kwamishinan ‘Yansanda ya tabbatar wa mazauna Kano cewa hukumar za ta ci gaba da kare rayuka da dukiyoyinsu, inda ya ce za su ci gaba da more zaman lafiya ba tare da fargaba ba. Haka kuma, hukumar ta bukaci jama’a da su rika kai rahoton duk wani abin da suka gani na zargi ta layukan gaggawa: 08032419754, 08123821575, ko 09029292926.

Rahotanni sun nuna karuwar ayyukan daba a Kano, musamman a cikin birnin, wanda ke janyo asarar rayuka da raunuka ga ‘yan daba da fararen hula.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ƴansanda Sun Fara Tsananta Ɗaukar Mataki Kan Ƴan Daba A Kano
  • Dakarun IRGC Sun Kakkabo Jirahen Yakin HKI Wadanda Ake Sarrafasu Daga Nesa A Lardin Zanjan
  • Dakarun Juyin Juya Halin Musulunci Na Iran Sun Kakkabo Jiragen Yakin Isra’ila Biyu Kirar F-35
  • Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Addu’ar Kwana 3 Don Samun Isasshen Abinci
  • Sudan Ta Zargi Janar Haftar Na Libiya Da Goyon Bayan ‘Yan Tawayen Kasarta Na Rapid Support Forces
  • Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
  • Masana Ilimin Nukiliyar Iran Sun Yi Shahada
  • An kashe masu garkuwa da mutane da kuɓutar da wasu
  • An kama ’yar Najeriya da laifin safarar ɗalibai 15 a Australia
  • Ƴansanda Sun Kama Shahararren Ɗan Damfarar Yanar Gizo A Bauchi