Aminiya:
2025-08-02@10:21:38 GMT

Lakurawa sun kashe jami’an Kwastam 2 a Kebbi

Published: 27th, March 2025 GMT

Wasu ’yan bindiga da ake zargin Lakurawa ne, sun kai har iyakar Bachaka da ke Ƙaramar Hukumar Argungu a Jihar Kebbi, inda suka kashe jami’an Kwastam biyu da wani mazaunin garin.

Harin ya faru ne kwana guda bayan da dakarun tsaro suka kashe wasu dakarun Lakurawa a yankin.

Ban sani ba ko zan tsaya takara a 2027 — Atiku Mutum 2,000 za su riƙa kamuwa da cutar HIV duk rana a duniya — MDD

Rundunar ’yan sandan Jihar Kebbi, ta tabbatar da faruwar harin, inda ta ce ba a tantance sunayen jami’an Kwastam da aka kashe ba.

“Eh, an kai hari, kuma ya yi sanadiyyar mutuwar jami’an Kwastam biyu da wani mazaunin Bachaka,” in ji kakakin rundunar, Nafiu Abubakar.

Bayan harin, Kwamishinan ’yan sandan jihar, CP Sani Bello, ya ziyarci wajen tare da tabbatar wa jama’a cewa hukumomin tsaro na aiki domin kama waɗanda suka kai harin.

“Waɗannan hare-hare na nuni da cewa miyagun suna raguwa saboda yawan farmakin da muke kai musu.

“Za mu ci gaba da yaƙar su har sai mun kawar da su gaba ɗaya,” in ji CP Bello.

Har yanzu, jama’a na cikin fargaba game da tsaro a yankunan kan iyaka, yayin da suke nuna damuwa kan yiwuwar sake kai musu hare-hare.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Kwastam Lakurawa jami an Kwastam

এছাড়াও পড়ুন:

An Yaba Da Kwazon Shugaba Bola Ahmad Tinubu

Masu ruwa da tsakin Arewa sun yaba da kwazon Tinubu, inda suka bukaci a kara karfafa gwiwar ‘yan kasa a taron Kaduna.

 

Masu ruwa da tsaki a Arewacin Najeriya sun yaba wa gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu bisa irin ci gaban da ta samu wajen cika alkawuran zabe, musamman a muhimman batutuwan da suka shafi tsaron kasa, samar da ababen more rayuwa, da sake fasalin tattalin arziki.

 

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun babban darakta na gidauniyar tunawa da Sardaunan Sakkwato Sir Ahmadu Bello, Engr. Abubakar Gambo Umar, kuma ya rabawa manema labarai a karshen taron tattaunawa na kwanaki biyu da aka gudanar a Arewa House, Kaduna.

 

Ya yaba wa gwamnatin Shugaba Tinubu saboda nuna gaskiya da kuma kyakkyawan aiki, yayin da ta bukaci ci gaba da jajircewa wajen tabbatar da daidaito, adalci, da hadin gwiwar yanki.

 

Mahalarta taron sun kuma yaba da irin ci gaban da gwamnatin ta samu kan manyan ayyuka irin su bututun iskar gas na AKK, da aikin hako mai na Kolmani, da kuma ayyukan noman rani na karkara wadanda ke amfana da al’ummar Arewa kai tsaye.

 

Ya tabbatar da cewa, kawancen ’yan kasa da na gwamnati na da matukar muhimmanci wajen dorewar dimokuradiyya, da hadin kan kasa, da kuma ci gaba mai dorewa.

 

Har ila yau, ya haifar da damuwa game da matsalolin da ke addabar yara da ba sa zuwa makaranta a Arewa da kuma gaggawar karfafa sarkar darajar noma don samar da ayyukan yi da samar da abinci.

 

Daga cikin muhimman kudurori, taron ya yi kira da a samar da tsare-tsare na yau da kullum na gwamnati da ‘yan kasa, a matakin kasa da na jihohi.

 

Har ila yau, ta ba da shawarar inganta harkokin zuba jari a fannin ilimi, musamman don magance tsarin Almajirai da kuma matsalar rashin makaranta da ke addabar Arewacin Nijeriya.

 

Mahalarta taron sun bayar da shawarar kara hadin gwiwa tsakanin gwamnatocin tarayya da na jihohi, da goyon bayan kishin kasa, dabarun da suka shafi al’umma don sauye-sauyen tattalin arziki da tsaro, tare da karfafa gwiwar kungiyoyin farar hula, na gargajiya, da shugabannin addinai da su kara taka rawa wajen bayar da shawarwarin manufofin jama’a.

 

Shugaban kungiyar gwamnonin Najeriya kuma gwamnan jihar Kwara Abdulrahman Abdulrazaq ne ya wakilci shugaba Bola Tinubu a wajen taron.

 

Mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima ya wakilci Dakta Aliyu Modibbo Umar, mai ba da shawara na musamman kan ayyuka na musamman, yayin da gwamnan jihar Kaduna, Sanata Uba Sani, ya kasance babban mai masaukin baki.

 

Gwamnan jihar Gombe kuma shugaban kungiyar gwamnonin jihohin Arewa, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya halarta a matsayin babban bako na musamman.

 

Manyan jami’an gwamnatin tarayya sun hada da Sakataren Gwamnatin Tarayya (SGF), Sanata George Akume, wanda ya jagoranci tawagar. Sauran manyan wadanda suka halarci taron sun hada da mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, mambobin majalisar ministocin tarayya, shugabannin hukumomin tsaro, da manyan jami’an tsaro daga Arewacin Najeriya.

 

A jawabin da ya gabatar, Farfesa Tijjani Mohammed Bande, ya bayyana yadda Najeriya ke da karfin gwiwa a cikin kalubale kamar rashin tsaro, talauci, da gibin ilimi.

 

Ya bukaci shugabannin Arewa da su tabbatar da muradun su a cikin tsarin kasa ta hanyar daidaitawa da ingantattun manufofin ci gaba masu amfani ga gamayya.

 

Babban zaman taron ya tattauna batutuwan da suka shafi kasa baki daya da suka hada da tsaro, shugabanci, farfado da tattalin arziki, noma, samar da ababen more rayuwa, da ci gaban bil Adama.

 

Adamu Yusuf

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Martani: Har yanzu muna ci gaba da yajin aiki — Ma’aikatan jinya  
  • An ceto mutum uku da aka yi garkuwa da su a Kebbi
  • Haaretz: Sojojin Isra’ila 7 ne suka kashe kansu a watan Yuli
  • Tinubu ya tsawaita wa’adin aikin shugaban hukumar Kwastam
  • Tinubu ya tsawaita wa’adin shugaban hukumar Kwastam
  • ZAMFARA: APC Ta Bukaci Gwamnatin Tarayya Ta Kawo Dauki Don Matsalar Tsaro Na Kara Tsananta
  • An Yaba Da Kwazon Shugaba Bola Ahmad Tinubu
  • Hare-hare: ’Yan bindiga sun raba mutum 5,000 da muhallansu a Katsina
  • Sojojin Yemen Sun Kai Zafafan Hare-Hare Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila Guda Uku  
  • Sojoji sun daƙile hari, sun kashe mayaƙan Boko Haram 9 a Borno