Ganin irin yawan kalubalen tattalin arziki da siyasa a Arewacin kasan nan ya sanya Tsohon Gwamnan Jihar Sokoto, Alhaji Attahiru Dalhatu Bafarawa, ya kaddamar da wata sabuwar kungiya mai taken Arewa Cohesion for Peace, Unity and Development Initiative.

 

An kaddamar da wannan kungiyoyi ce a wajen wani babban taro da aka gudanar a Arewa House, Kaduna, inda manyan baki da mahalarta daga sassa daban-daban na Arewa suka halarta.

 

A yayin taron, Bafarawa wanda shi ne Shugaban Kwamitin Amintattu na tafiyar, ya bayyana wannan mataki a matsayin sabon hanyar da za ta yi maganin baraka da inganta fahimtar juna da kuma karfafa ci gaban mai dorewa a yankin Arewa.

 

Ya ce Arewacin Najeriya na fuskantar kalubale da dama da suka hada da rikice-rikicen al’umma, rashin tsaro, zaman kashe wando a tsakanin matasa da wariyar tattalin arziki da kuma lalacewar dabi’u da da suka hade mutanen yankin a da.

 

Tsohon Gwamnan jihar Sokoton, yace manufar tafiyar ita ce samar da zaman lafiya da fahimtar juna tsakanin al’ummomi daban-daban a Arewa, tare da samar da hanyoyi na tattaunawa da sulhu da kuma warware rikice-rikice.

 

Bafarawa ya jaddada cewa tafiyar za ta maida hankali kan matasa, da aiki tare da gwamnatoci da Sarakuna da Malaman addini da kungiyoyin masu zaman kansu da abokan hulɗa na kasa da kasa, don gina Arewa mai aminci da karfi da kuma adalci ga kowa.

 

Ya bayyana cewa tafiyar ba ta da nasaba da siyasa, kuma babu niyyar mayar da ita jam’iyyar siyasa ko goyon bayan kowace jam’iyya. Ya ce burinsu ya wuce siyasa, domin suna son aiki da kowa muddin yana da burin ciyar da Arewa da Najeriya gaba. Ya kara da cewa su na bude wajen aiki da kowace kungiya da ke da manufofi irin nasu.

 

Duk da kasancewar tafiyar ba ta siyasa ba ce, Bafarawa ya bayyana cewa ’yan tafiyar na da ’yancin shiga harkokin siyasa a matsayin kansu ba tare da nasaba da tafiyar ba.

 

Bafarawa ya kuma sanar da cewa an kammala tsara wata cikakkiyar tsarin taswira (blueprint) da ke kunshe da hanyoyin farfado da Arewacin Najeriya, wadda aka samo daga bincike da nazari mai zurfi kan damar yankin.

 

A nasa jawabin, Darakta Janar na tafiyar, Dr. Abdullahi Idris, ya bayyana cewa an kirkiro tafiyar ne sakamakon tabbacin cewa kalubalen da ke fuskantar yankin ba za su warware sai da hadin gwiwa da fahimtar juna da tsare-tsaren ci gaba da zaman lafiya.

 

Dr. Idris ya bayyana tafiyar Arewa Cohesion Initiative a matsayin mafita mai muhimmanci da dacewa da lokaci, wacce ta ta’allaka ne a kan ginshikai uku: gina zaman lafiya, dunkulewar Arewa da ci gaban da za a iya jurewa.

 

Ya shawarci masu ruwa da tsaki su kasance masu hangen nesa wajen magance matsalolin yankin, yana mai jaddada cewa wadannan matsaloli ba a haifar da su cikin dare daya ba, kuma ba za su warware cikin dare daya ba. Sai dai da hakuri, hadin kai da jajircewa, ana iya samun sauyi mai ma’ana.

 

Shugaban taron kuma Janar mai murabus, Jon Temlong, ya jinjinawa Bafarawa bisa jajircewarsa wajen ci gaban kasa bayan barin siyasa. Ya ce wannan tafiya tana dauke da dabi’u na gaskiya da ke bayyana Arewacin Najeriya — zumunci, adalci da hadin kai.

 

Janar Temlong ya ce shugabancin tafiyar yana dauke da fatan al’umma da dama, yana mai bayyana cewa wannan kaddamarwa na iya zama sauyi mai muhimmanci a kokarin Arewacin Najeriya na neman zaman lafiya da ci gaba mai dorewa.

 

Taron ya samu halartar jama’a da dama daga sassa daban-daban na Arewacin Najeriya, alamar goyon baya da hadin kai ga wannan tafiya.

COV: Adamu Yusuf

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Arewa Cohesion Initiative Arewa Bafarawa Kaddamar KalubalenYankin Kungiya

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Namadi Ya Bukaci Hadin Gwiwar Hukumar Kwastam Don Farfado Da Yankin Kasuwanci Na Maigatari

Gwamna Malam Umar Namadi na Jihar Jigawa ya jaddada kudirin gwamnatinsa na farfado da harkar kasuwanci mara shinge a Maigatari, wanda ya bayyana a matsayin muhimmin ginshikin bunkasar tattalin arziki, kasuwanci da masana’antu a jihar.

Ya bayyana hakan ne yayin wata ganawa da Kwamandan Yankin K da Jigawa na Hukumar Kwastam ta Najeriya, Kwamanda Dalhat Abubakar, wanda ya kai masa ziyarar ban girma a Fadar Gwamnati da ke Dutse.

Gwamna Namadi ya taya Kwamanda Abubakar murnar nadin nasa, tare da yaba wa hukumar Kwastam bisa goyon bayan manufofin cigaban jihar Jigawa, musamman wajen farfado da aikin Maigatari da aka yi watsi da shi.

Ya nuna godiya bisa goyon bayan  Kwamandan ya bayar, tare da yabawa da rahotannin da ke nuna yadda yake hada kai da tawagar tattalin arzikin jihar kan aikin.

Gwamnan ya bayyana tarihin  Maigatari Free Trade Zone, yana cewa ko da yake an kafa yankin fiye da shekaru 25 da suka wuce, an bar shi kara zube ba tare da cimma manufarsa ba.

Ya ce gwamnatinsa ta dauki matakai masu muhimmanci domin farfado da shi.

A cewarsa, an biya kudaden lasisi na doka, an yi shirin sake matsuguni ga mazauna yankin, kuma ana ci gaba da tattaunawa da masu zuba jari domin fara aiki da yankin.

Ya jaddada muhimmancin hadin gwiwa da hukumomin tarayya kamar Hukumar Kwastam don tabbatar da cewa yankin ya fara aiki gaba daya.

A nasa jawabin, Kwamanda Abubakar ya tabbatar da cewa Hukumar Kwastam ta shirya tsaf don fara aiki a Maigatari nan take, yana mai cewa sauran matsalolin da ke akwai na harkokin gudanarwa ne da na kayayyakin aiki, kuma za a iya magance su cikin sauki.

Ya yaba da jajircewar tawagar tattalin arzikin Jigawa, yana bayyana su a matsayin kwararru da kuma masu cikakken biyayya ga hangen nesan gwamna dangane da Maigatari.

Kwamanda Abubakar ya kuma jaddada irin fifikon da yankin Maigatari ke da shi, yana cewa kasancewarsa kusa da iyaka na ba shi gagarumar dama fiye da sauran yankuna, har da manyan cibiyoyin kasuwanci irin su Kano.

Ya bukaci ci gaba da hadin gwiwa tsakanin dukkan masu ruwa da tsaki don shawo kan sauran kalubale da kuma fitar da cikakken alfanu daga yankin.

A karshe, Gwamna Namadi ya tabbatar da cewa gwamnatinsa a shirye take ta dauki matakan da suka dace da shawarwari da tallafin da ake bukata don tabbatar da cewa Maigatari ya fara aiki gaba daya, tare da yin tasiri ga tattalin arziki.

 

Usman Muhammad Zaria 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  HKI Tana Cigaba Da Yi Wa Mutanen Gaza Kisan Kiyashi
  • Gwamna Namadi Ya Bukaci Hadin Gwiwar Hukumar Kwastam Don Farfado Da Yankin Kasuwanci Na Maigatari
  • Babban Kwamandan Sojin Iran Ya Bayyana Cewa Iran Ta Koyawa Gwamnatin Isra’ila Hankali
  • Sauye-sauyen Tinubu Suna Taimaka Wa Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya — Minista
  • Trump Ya Kakabawa Wata Jami’in MDD Takunkumi Bayan Ta Fallasa Laifukan HKI Da Hannun Amurka A Ciki
  • Yara miliyan 5.4 na fama da karancin abinci a jihohin arewa 9 – Red Cross
  • Za A Horas Da Jami’an Tsaron Sakkwato, Kaduna Da Benue Sabbin Dabarun Aiki
  • Gamayyar ‘Yan Adawa Sun Kaddamar ADC A Gombe  
  • ‘Abin da zai sa APC ba za ta taɓa mantawa da Ganduje ba’