Zamu Tabbatar Ingantuwar Depon Sojoji Na Zaria – Ministan Tsaro Badaru
Published: 27th, March 2025 GMT
Ministan Tsaro, Mohammed Badaru Abubakar ya yi alkawarin inganta sansanin horas da kuratan sojoji dake Zaria wato Depot domin baiwa hukumar Soji damar ci gaba da aikin horaswa a wajen.
Ministan ya yi wannan alkawarin ne a lokacin da ya kai ziyarar tantance sojojin Najeriya da ke Chindit Cantonment a Zariya.
Ministan ya kuma ce, ma’aikatar tsaro ba za ta bar wani abu ba, wajen tabbatar da cewa makarantar firamare ta Chindit ta samu ingantuwar kayan aiki don dacewa da tsarin zamani a matsayin hanyar kara kwarin gwiwa na hafsoshi da sojoji na Kantoment da ke amfana da wajen.
Ya kara da cewa ofishin sa zai hada kai da gwamnatin jihar Kaduna domin ganin an kammala makarantar sakandare ta Chindit.
Ministan ya kuma yi alkawarin taimakawa wajen hakar wasu rijiyoyin burtsatse masu amfani da hasken rana domin kara inganta rijiyoyin burtsatse da ke cikin Depot din domin rage kalubalen da ke tattare da samar da ruwan sha a yankin.
Da yake jawabi tun da farko, kwamandan, Depot, Manjo Janar Ahmed Mohammed ya gode wa ministan bisa wannan ziyara, sannan ya kuma sanar da shi yadda babban hafsan sojin kasa, Laftanar-Janar Olufemi Oluyede ya yi don magance kalubalen da ke fuskantar Depot din.
Ya kuma bayyana fatan cewa wannan hadin gwiwa zai sanya Depot a kan hanyar da ta dace don ganin ta cika aikinta na samarda sojojin Nijeriya.
Kwamandan ya bada tabbacin cewa za a kula da jin dadin ma’aikata da wadanda aka dauka yadda ya kamata domin tabbatar da cewa hukumar ta samu cikakkiyar damar cimma muradun Najeriya.
REL/HALIRU HAMZA
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Sabon Tsarin Kula Da Lafiyar Mata Masu Juna Biyu Da Kananan Yara
Gwamnatin Jigawa ta amince da sabon tsarin ka’idojin aiki domin aiwatar da shirin kula da lafiyar mata masu juna biyu, da jarirai da ƙananan yara kyauta a cibiyoyin lafiya na jihar.
Kwamishinan Yaɗa Labarai, Alhaji Sagir Musa Ahmed, ya bayyana haka bayan zaman majalisar zartarwa da aka gudanar a gidan gwamnati Dutse.
Ya ce ka’idojin za su taimaka wajen inganta nagartar hidima, fayyace karewar ma’aikata, da kuma tabbatar da gaskiya, da bin doka da tsari a asibitoci.
Kwamishinan ya ƙara da cewa matakin ya dace da manufar gwamnatin jihar na rage mace-macen mata da yara da kuma tabbatar da samun ingantacciyar kulawa ga kowa.
Ya ce za a fara aiwatar da tsarin nan take, tare da horas da shugabannin asibitoci da cibiyoyin lafiya na ƙananan hukumomi domin cimma nasarar shirin .
Usman Muhammad Zaria
—
Kana so in ƙara ɗan salo na labarin jarida (irin rubutun kafafen yaɗa labarai) ko a barshi haka cikin sauƙin bayani?