Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita
Published: 11th, July 2025 GMT
Mataimakin babban magatakardan MDD, kana sakataren zartarwa na kwamitin tattalin arzikin Afirka Claver Gatete, ya bayyana cewa, kasar Sin aminiya ce da kasashen Afirka za su iya dogaro da ita.
Gatete ya bayyana hakan ne a ranar Talata, yayin da ya karbi takardar wakilcin kasa daga sabon wakilin kasar Sin a kwamitin tattalin arzikin Afirka na MDD, kana shugaban tawagar jakadun kasar Sin dake kungiyar tarayyar kasashen Afirka ta AU Jiang Feng a birnin Addis Ababan kasar Habasha, mazaunin kwamitin na tattalin arzikin Afirka na MDD.
A yayin ganawarsu, Claver Gatete ya taya Jiang Feng murnar gudanar da sabbin ayyuka, ya kuma yi fatan karfafa hadin gwiwa da kasar Sin, domin ba da taimako ga bunkasa hadin gwiwa tsakanin kasashen Afirka da kasar Sin. Haka kuma, ya yi matukar jinjina ga manufar cire haraji kan hajojin Afirka da kasar Sin ta fidda.
A nasa bangare kuwa, Jiang Feng ya ce, kasar Sin tana fatan hada kai da kwamitin tattalin arzikin Afirka, wajen aiwatar da sakamakon da aka cimma a taron koli na dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da Afirka na Beijing, tare da gina makomar al’ummun Sin da Afirka ta bai daya. (Mai Fassara: Maryam Yang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: tattalin arzikin Afirka
এছাড়াও পড়ুন:
Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Lin Jian, ya ce alkaluman baya bayan nan da aka fitar cikin Mujallar Economist, sun shaida yadda hada-hadar cinikayyar fitar da hajoji ta kasar Sin ke kara bunkasa cikin sauri a shekarar nan ta bana, inda fannin ke samun karuwar abokan hulda, da daidaiton matsayi cikin tsarin samar da hajojin masana’antu na kasa da kasa.
Kakakin ya kara da cewa, kasashen duniya suna maraba da hajojin kasar Sin, kuma yakin ciniki da haraji ba su yi wani babban tasiri kan kasar Sin ba. A fannin hada-hadar cinikayya, sanya shinge ba alama ce ta karfin gwiwa ba, kuma katangar da Amurka ke ginawa kanta, daga karshe za ta illata karfinta ne.
Lin Jian, wanda ya bayyana hakan yayin taron manema labarai da aka saba gudanarwa a yau Laraba, ya ce yayin da ake fama da yanayi mai sarkakiya, da sauye-sauye masu maimaituwa daga ketare, cinikayyar waje ta Sin na gudana lami lafiya, cike da karfin juriya da babban karsashi.
Hakan a cewarsa, ya shaida gazawar yakin haraji da cinikayya wajen girgiza fifikon da Sin ke da shi, a fannin raya masana’antun sarrafa hajoji da kasar ta gina a tsawon lokaci. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp