Majalisar Limaman Turai Ta Nesanta Kanta Daga Wadanda Su Ka Ziyarci HKI
Published: 10th, July 2025 GMT
Majalisar limaman musulmin nahiyar turai ta fitar da wani bayani da ta nesanta kanta daga wasu mutane da su ka kai ziyarar HKI tare da bayyana kansu a matsayin limamai daga kasashen turai, tana mai cewa, ko kadan ba su wakiltar al’ummar musulmin da suke cikin nahiyar ta turai.
A ranar Litinin din da ta gabata ne dai ofishin shugaban HKI Ishaq Herzog ya fitar da bayani da a ciki yake cewa; A ofis dinsa dake birnin Kudus ya karbi bakuncin limaman musulmi daga kasashen Faransa,Belgium, Holland, Italia da kuma Birtyaniya.
Ofishin majalisar limaman musulmin na turai, mai matsugunni a Faransa ya bayyana ziyarar mutanen zuwa Isra’ila da cewa, tana da daure kai, haka nan kuma lokacin da aka yi ta.”
Majalisar ta limaman turai din ta yi kira ga dukkanin ‘yantattu a duniya da su kasance a tare da al’ummar Falasdinu da ake zalunta, domin ganin an kawo karshen kisan kiyashin da sojojin mamaya suke yi musu.
Bugu da kari majalisar ta ce, wannan ziyarar tana nuni da yadda wadanda su ka yi ta ba su da lamiri na ‘yan’adamtaka da rashin riko da mafi karancin koyarwar musulunci ta yin kira da a taimaki gaskiya.”
Majalisar limaman na Turai ta kuma kara da cewa; ziyarar wani kokari ne na wanke ‘yan mamaya, kuma cin amanar Allah da manzon Allah ne da jinanen raunana.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: Majalisar limaman
এছাড়াও পড়ুন:
HOTUNA: Obi ya ziyarci iyalin Ɗantata don yi musu ta’aziyya
Ɗan takarar Shugaban Ƙasa na jam’iyyar LP a zaɓen 2023, Peter Obi, ya ziyarci iyalin marigayi, Alhaji Aminu Dantata a Jihar Kano, don yi musu ta’aziyya.
Obi, ya bayyana cewa ya yi matuƙar baƙin ciki da rasuwar Alhaji Ɗantata, inda ya bayyana shi a matsayin “uba ga kowa.”
An gabatar da Ganduje a matsayin shugaban kwamitin hukumar FAAN 2027: Idan ADC na son lashe zaɓe dole ta bai wa ɗan Arewa takara — OkonkwoYa yaba yadda Ɗantata ya zama babban attajiri kuma ya taimaka wa mutane da dama suka samu nasara a rayuwarsu.
Ya ce Ɗantata ya taka muhimmiyar rawa wajen ci gaban Najeriya.
“Mun zo nan yau don jimami tare da iyalinsa da kuma ɗaukacin ‘yan Najeriya, saboda wannan babban rashi ne,” in ji Obi.
“Alhaji Aminu Dantata ba mai kuɗi ba ne kawai, ya taimaka wa wasu wajen cimma nasararsu a rayuwa.
“Ya kula da mutane sosai kuma ya zama kamar uba ga mutane da dama.”
Obi, ya bayyana Ɗantata a matsayin mutum mai tausayi da kishin ƙasa.
Ya ce mutuwarsa ta shafu al’amura da dama a wannan zamani.
Haka kuma, Obi ya yi addu’ar Allah Madaukakin Sarki Ya gafarta masa, ya saka masa da alheri, ya kuma albarkaci iyalinsa.
“Rayuwarsa abin koyi ce. Ba wai kasuwanci kawai ya yi ba, ya zuba jari a cikin al’umma. Abin da ya bari zai ci gaba da zama abin koyi.
“Allah Ya albarkaci wannan gida, ya albarkaci Najeriya baki ɗaya,” in ji Obi.
Alhaji Aminu Ɗantata fitaccen ɗan kasuwa ne luma mai taimakon jama’a daga Arewacin Najeriya.
Ya rasu yana da shekarau 94.
Mutane da dama daga sassa daban-daban na ƙasar nan sun yi alhini bisa gudunmawar da ya bayar a harkar tattalin arziƙi da taimakon jama’a.
Ga hotunan ziyarar a ƙasa: