Leadership News Hausa:
2025-07-31@12:24:45 GMT

Wakilin Sin: Dole Ne A Mutunta Hakki Mai Tushe Na Palasdinawa

Published: 27th, March 2025 GMT

Wakilin Sin: Dole Ne A Mutunta Hakki Mai Tushe Na Palasdinawa

Wakilin dindindin na kasar Sin a ofishin MDD dake Geneva da sauran kungiyoyin kasa da kasa dake Switzerland Chen Xu, ya gabatar da jawabi a jiya Laraba, yayin taro na 58 na kwamiti mai kula da harkokin kare hakkin bil Adama na MDD, don bayyana ra’ayin kasar Sin kan halin da Palasdinu da Isra’ila ke ciki.

A cewarsa, daruruwan fararen hula sun yi asara sakamakon hare-hare ta sama da aka kaiwa zirin Gaza, kuma Sin na matukar adawa da hakan, tare da bayyana bacin ranta game da tabarbarewar matakin tsagaita bude wuta a wurin, wanda aka dauka bayan an sha matukar wahala. Ya ce abin da aka sa gaba cikin gaggawa shi ne kaucewa daukar ko wane irin mataki dake iya tsananta halin da ake ciki, ta yadda za a dakile barkewar bala’in keta hakkin bil Adama da jin kai mafi tsanani.

Chen ya kara da cewa, Sin na adawa da tilasawa fararen hula ficewa daga zirin Gaza. Kana tana goyon bayan shirin farfado da zaman lafiya a Gaza, wanda kasashen Larabawa ciki har da Masar suka gabatar, da farfado da zirin Gaza bisa ka’idar “Barin Palasdinawa su gudanar da harkokinsu da kansu” ba tare da bata lokaci ba.

Har ila yau, Chen ya jaddada cewa, ba za a iya warware batun Palasdinu ba, har sai an koma hanyar da ta dace, wato manufar “Kafa kasar Palasdinu da Isra’ila”. (Amina Xu)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Kasar Iran Ta Musanta Yin Katsalandan A Tattaunawar Neman Tsagaita Bude Wuta A Gaza

Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta musanta zargin yin katsalandan a tattaunawar tsagaita bude wuta a Gaza

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran, Ismail Baqa’i, ya musanta zargin katsalandan din Iran a tattaunawar tsagaita bude wuta a Gaza.

A yayin da yake amsa tambaya game da ikirarin da shugaban kasar Amurka ya yi na cewa Iran na tsoma baki a shawarwarin tsagaita bude wuta a zirin Gaza, ya ce: Jamhuriyar Musulunci ta Iran tare da dukkan kasashen duniya tana yin kakkausar suka kan kisan gillar da ake yi a Gaza tare da goyon bayan duk wani tsari da zai kai ga dakatar da aikata laifuka da kuma rage radadin wahalhalun da al’ummar Gaza suke ciki.

Baqa’i ya jaddada cewa; Masu yin shawarwarin Hamas sun fahimci bukatar neman cimma muradun al’ummar Gaza da ake zalunta ta hanyar da ta dace, kuma ba sa bukatar shiga tsakani na bangarori na uku dangane da hakan.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar ta Iran ya yi la’akari da katsalandan din Iran a cikin shawarwarin da suka dace da cewa ba shi da tushe balle makama, yana mai jaddada cewa irin wadannan zarge-zarge wani nau’i ne na neman tauyaye hakki da gujewa hakkin da ya rataya a wuyar mutum da kokarin Amurka na gujewa duk wani mugun aiki da gwamnatin ‘yan sahayoniyya ta aikita kan al’ummar Falasdinu, da suka hada da kisan fararen hula 60,000 da ba su ji ba ba su gani ba, da suka hada da mata da kananan yara da kuma killace Zirin Gaza tsawon watanni. Da hana shigar agajin jin kai da kuma kashe fararen hula da ke fama da yunwa da kishirwa a tarkon kisa a wuraren da ake kira cibiyoyin rarraba kayan agaji da wata cibiyar Amurka ta kafa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Samar da makamashi mai tsafta na zamani shi ne fatanmu — Guterres
  • Tawagar Iran Ta Fice A Taron Majalisun Dokokin Kasashen Duniya A Lokacin Jawabin Wakilin Isra’ila
  • Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega
  • Amincewa Da Kasar Falasɗinu: Birtaniya Ta Gindaya Wa Isra’ila Sharuɗɗa
  • Birtaniya Ta Yi Barazanar Amincewa Da Kasar Falasdinu A Watan Satumba Idan Yanayin Gaza Bai Canza Ba
  • Gwamnatin Katsina Ta Fara Bayar Da Maganin Zazzabi Kyauta A Asibitoci
  • Kasar Iran Ta Musanta Yin Katsalandan A Tattaunawar Neman Tsagaita Bude Wuta A Gaza
  • Wakilin Gidan Talabijin Na Al-Alam Ya Bayyana Yadda Shi Da Iyalansa Suka Rayu Kwanaki Biyu Babu Abinci A Gaza
  • Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa
  • Shugaban Kasar Masar Ya Roki Trump Ya Kawo Karshen Yaki A Gaza