Leadership News Hausa:
2025-05-01@04:11:31 GMT

Wakilin Sin: Dole Ne A Mutunta Hakki Mai Tushe Na Palasdinawa

Published: 27th, March 2025 GMT

Wakilin Sin: Dole Ne A Mutunta Hakki Mai Tushe Na Palasdinawa

Wakilin dindindin na kasar Sin a ofishin MDD dake Geneva da sauran kungiyoyin kasa da kasa dake Switzerland Chen Xu, ya gabatar da jawabi a jiya Laraba, yayin taro na 58 na kwamiti mai kula da harkokin kare hakkin bil Adama na MDD, don bayyana ra’ayin kasar Sin kan halin da Palasdinu da Isra’ila ke ciki.

A cewarsa, daruruwan fararen hula sun yi asara sakamakon hare-hare ta sama da aka kaiwa zirin Gaza, kuma Sin na matukar adawa da hakan, tare da bayyana bacin ranta game da tabarbarewar matakin tsagaita bude wuta a wurin, wanda aka dauka bayan an sha matukar wahala. Ya ce abin da aka sa gaba cikin gaggawa shi ne kaucewa daukar ko wane irin mataki dake iya tsananta halin da ake ciki, ta yadda za a dakile barkewar bala’in keta hakkin bil Adama da jin kai mafi tsanani.

Chen ya kara da cewa, Sin na adawa da tilasawa fararen hula ficewa daga zirin Gaza. Kana tana goyon bayan shirin farfado da zaman lafiya a Gaza, wanda kasashen Larabawa ciki har da Masar suka gabatar, da farfado da zirin Gaza bisa ka’idar “Barin Palasdinawa su gudanar da harkokinsu da kansu” ba tare da bata lokaci ba.

Har ila yau, Chen ya jaddada cewa, ba za a iya warware batun Palasdinu ba, har sai an koma hanyar da ta dace, wato manufar “Kafa kasar Palasdinu da Isra’ila”. (Amina Xu)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa da Mutane 12 Da Masu Sayar da Makamai 3 A Taraba Da Kaduna

A Kaduna, an kama wasu mutane uku da ake zargin masu garkuwa da mutane ne, ciki har da wani da ya ce ya koma jihar ne domin kafa sabuwar ƙungiya bayan an kama abokan aikinsa a Kwara.

Haka kuma, an kama wasu biyu da ke ɗauke da bindigogi.

‘Yansanda sun gano makamai da dama, ciki har da bindigogi ƙirar AK-47 da AK-49, da kuma wasu makamai da aka ƙera a gida.

Wannan aiki na daga cikin ƙoƙarin gwamnati na yaƙar garkuwa da mutane da safarar makamai a faɗin ƙasar.

Kakakin rundunar, Olumuyiwa Adejobi, ya ce ana ci gaba da bincike, kuma za a gurfanar da waɗanda ake zargi a kotu da zarar an kammala binciken.

Ya kuma yaba da goyon bayan da al’umma da jami’an tsaro suka bayar wajen nasarar kama su.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwastam Ta Kama Jirage Marasa Matuka Da Sauran Kayayyaki Da Darajarsu Ta Haura Naira Biliyan 921 A Legas
  • An kashe Falasdinawa kusan 30 a wani sabon kisan kiyashin Isra’ila a Gaza
  • Saudiya Ta Yi Allawadai Da Kissan Kiyashin Da HKI Take Yi A Gaza A Gaban Kutun ICJ
  • ‘Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa da Mutane 12 Da Masu Sayar da Makamai 3 A Taraba Da Kaduna
  • NEMA Ta Karɓi ‘Yan Nijeriya 203 Da Suka Maƙale A Libya
  • Talauci Da Rashin Ilimi Ne Ya Sa Ayyukan Boko Haram Ke Dawowa – Gwamnan Yobe
  • Nazarin CGTN: Ana Kara Bayyana Rashin Gamsuwa Da Sabuwar Gwamnatin Amurka Daga Ciki Da Wajen Kasar
  • Kungiyar Amnesty International Ta Kafa Hujja Kan Ta’asar’Yan Sahayoniyya A Gaza
  • Makafi 37 Sun Zana Jarabawar JAMB A Bauchi
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Ci Gaba Da Killace Gaza Da Kashe Mutane, Laifi Ne Da Ba A Taba Yin Irinsa Ba