Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

A yau Talata ne firaministan Sin Li Qiang, ya gana da kakakin majalisar wakilan tarayyar Najeriya Tajudeen Abbas, wanda ya isa birnin Shanghai don halartar baje kolin CIIE karo na takwas.

Yayin zantawarsu, Li Qiang ya bayyana aniyar kasar Sin ta karfafa salon wanzar da ci gaba bisa manyan tsare-tsare tare da Najeriya, da zage damtse wajen aiwatar da wasu muhimman matakai goma na bunkasa kawance tsakanin Sin da kasashen nahiyar Afirka, da hada hannu wajen gina shawarar “Zira Daya Da Hanya Daya” mai inganci, da bunkasa matakin hadin gwiwa a sassan gargajiya, da fadada hadin gwiwa a sabbin masana’antu, da kara kyautata gina tattalin arziki da zamantakewar al’ummun sassan biyu.

Li Qiang ya kara da cewa, akwai bukatar kasashen biyu su karfafa tsare-tsare, da hadin gwiwa a fannin gudanar da cudanyar mabambantan sassa, karkashin irinsu hadakar kasashen BRICS, da MDD, da yayata hadin kai, da inganta karfin kasashe masu tasowa.

A nasa tsokacin, Tajudeen Abbas ya ce Najeriya na rike da manufar nan ta Sin daya tak a duniya, kuma a shirye take ta karfafa musayar kwarewar jagoranci tare da Sin, da fadada hadin gwiwa a sassa da dama, kamar tattalin arziki da cinikayya, da samar da ababen more rayuwa, da makamashi, da al’adu, tare da ci gaba da daga cikakkiyar dangantaka bisa manyan tsare-tsare tsakanin Najeriya da Sin zuwa babban matsayi. (Saminu Alhassan)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa November 4, 2025 Daga Birnin Sin Shugaban Xi Ya Gana Da Firaministan Rasha November 4, 2025 Daga Birnin Sin Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin November 3, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya
  • Zulum Ya Raba Motocin Sintiri 63 Ga Hukumomin Tsaro A Borno
  • Natasha Ta Zargi Akpabio Da Sanya Jami’an Tsaro Su Ƙwace Mata Fasfo A Filin Jirgin Saman Abuja 
  • Ribadu Ya Gana Da Manyan Hafsoshin Tsaron Najeriya kan barazanar Trump
  • Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 
  • Kwamishinan Ƴansanda Na Kano Ya Karrama Sabbin Jami’an Da Aka Ƙara Wa Matsayi
  • Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga 19, Sun Ƙwato Makamai A Kano
  • Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar
  • Barazanar Amurka Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya: Tinubu Da Trump Za Su Gana Kwanan Nan — Bwala
  • Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori