Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp.

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Corruption

এছাড়াও পড়ুন:

Hukumar Kiyaye Hadura Ta Kasa Za Ta Aiki Da ‘Yan Jarida A Kano

Hukumar kiyaye hadurra ta kasa (FRSC) reshen jihar Kano, ta bayyana kudurinta na kara zurfafa dangantakarta da kungiyar ‘yan jarida ta kasa NUJ reshen jihar Kano.

 

Wannan alkawari ya fito ne daga bakin kwamandan sashin, Kwamandan Corps Muhammad Bature, a lokacin da yake karbar sabbin shugabannin majalisar a hedikwatar hukumar FRSC da ke Kano.

 

Sabbin shugabannin kungiyar masu aiko da rahotanni ta NUJ sun ziyarci hukumar FRSC ta Kano domin taya rundunar murna kan kokarin da take yi na inganta hanyoyin kiyaye hadurra da kuma gano sabbin hanyoyin hadin gwiwa.

 

Kwamandan sashin ya yi maraba da ziyarar, inda ya bayyana ta a matsayin wata babbar alama ta tabbatar da ci gaba da hadin gwiwa tsakanin FRSC da NUJ.

 

Ya bayyana jin dadinsa na yin aiki kafada da kafada da NUJ domin inganta moriyar juna.

 

Kwamandan sashin ya kuma gayyaci mambobin Kungiyar da su shiga rundunar FRSC Special Marshal Corps a matsayin masu aikin sa kai. Wannan shiri na da nufin tallafa wa kokarin da hukumar ta ke yi a fadin kasar na rage hadurran ababen hawa da asarar rayuka.

 

Da yake mayar da martani ga kwamandan sashin, zababben shugaban kungiyar ta Chapel, Murtala Adewale, ya ce makasudin ziyarar shi ne don kara tabbatar da alakar da ke tsakanin FRSC da jami’an kungiyar.

 

Adewale ya bayyana kwarin gwiwarsa na cewa FRSC zai bayar da dandali fadakarwa da zai kara wayar da kan jama’a kan kiyaye hanyoyin mota a fadin Kano da ma wajen.

 

 

Abdullahi Jalaluddeen Kano

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Muna so a kafa doka ta bincikar yadda ’yan Nijeriya ke tara dukiya — EFCC
  • Dangote Ya Yaba Wa Tinubu Kan Samar Da Ababen More Rayuwa A Nijeriya
  • EFCC Ta Kama Ƴan Ƙasashen Waje 146 Kan Laifukan Zambar Kuɗaɗe
  • Babu Wanda Ya Buƙaci Atiku Ka Da Ya Yi Takara A 2027 – ADC
  • Amurka Ta Tsaurara Matakan Bai Wa ‘Yan Nijeriya Biza
  • Hukumar Kiyaye Hadura Ta Kasa Za Ta Aiki Da ‘Yan Jarida A Kano
  • ‘Yansanda Sun Kuɓutar Da ‘Yan Ghana 19 Da Aka Yaudare Su Zuwa Nijeriya
  • ASUU Ta Tsunduma Yajin Aiki A Faɗin Nijeriya
  • Nijeriya Ba Ta Da Sha’awar Yin Gwajin Makamin Nukiliya — Shettima