HausaTv:
2025-09-17@23:17:44 GMT

 HKI Tana Cigaba Da Yi Wa Mutanen Gaza Kisan Kiyashi

Published: 10th, July 2025 GMT

Sojojin Sahayoniya suna ci gaba da yi wa mutane Gaza kisan kiyashi a kwana na 643 a jere.

Sojojin sahayoniyar suna amfani da dukkanin kayan yaki da su ka hada jiragen masa masu matuki da marasa matuki, da kuma manyan bindigogi.

Tun da safiyar yau Alhamis ne dai sojojin HKI su ka fara kai hare-hare da tankokin yaki bayan kutsawarsu cikin yankin “Bi’irut-Turki” da “maslakh” dake kudancin Khan-Yunus.

Tankokin sun rika bude wuta akan mai uwa da wabi da gidajen mutane a cikin yankin, da hakan ya yi sanadiyyar jikkatar mutane da yawa.”

Majiyar Falasdinawa ta tabbatar da shahadar mutane 16, da su ka hada mata da kananan yara a wuruin da suke jiran karbar abincin agaji a shataletalen al-Dhayyarah, a Deir-Balah dake tsakiyar birnin Gaza.

A gabashin birnin Gaza kuwa, sojojin mamayar sun kara rusa gidaje masu yawa, da ya yi sanadiyyar shahadar Falasdinawa 4 a cikin iyalai guda na Abu Jild.

Har ila yau, majiyar ta ce, wani karamin yaro mai suna Yusuf Hassan al-Ammur ya yi shahada sanadiyyar raunukan da ya samu a jiya da ‘yan sahayoniyar su ka kai hare-haren da su ka kwantar da shahidai 4.

A sansanin ‘yan hijira na “Nusairat” kuwa dake tsakiyar Gaza wani Bafalasdine mai suna; Abduljalil Khitab, da Akram al-Dairawi, sun yi shahada saboda harin da sojojin mamayar su ka kai wa motar da suke ciki. A tsakiyar daren jiya ma dai wasu Falasdinawan 5 su ka yi shahada a yankin Mawasi dake yammacin Khan-Yunus.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

 

A yayin samamen, kakakin ‘yansandan Neja ya ce an kama mutane shida a wurin da ake hakar ma’adinan yayin da wasu kuma suka tsere.

 

Abiodun ya bayyana sunayen wadanda ake cafken da Aliyu Rabiu, Samaila Ibrahim, Sadiku Auwal, Ibrahim Babangida, Musa Adamu da Sani Hassan.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kama ɗaya daga cikin manyan kwamandojin IPOB
  • ‘Yansanda Sun Kama Mutane 6 Kan Zargin Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
  •  Gaza: HKI Tana Ci Gaba Da Yi Wa Falasdinawa  Kisan Kiyashi A Gaza
  • Kwamitin bincike na MDD ya zargi Isra’ila da aikata “kisan kare dangi” a Gaza
  • Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire
  • Espania Ta Soke Cinikin Makamai Na EUR Miliyon 700 Da HKI Saboda Kissan Kiyashi A Gaza
  • Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”
  • Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi
  • An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar
  • Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada Sakamakon Kisan Kiyashin ‘Yan Sahayoniyya A Gaza Ya Kusaci 65,000