Majalisa ta buƙaci a rage kuɗin data don sauƙaƙa wa ’yan Najeriya
Published: 27th, March 2025 GMT
Majalisar Dattawa, ta buƙaci Ma’aikatar Sadarwa da ta yi aiki tare da kamfanonin sadarwa domin rage kuɗin data, ta yadda kowa zai iya samun Intanet mai sauƙi a Najeriya.
A zaman majalisar na ranar Laraba, Sanata Asuquo Ekpenyong (APC – Kuros Riba), ya nuna damuwa kan yadda farashin data ya ƙaru da kusan kashi 200.
Ya ce ƙarin yana hana mutane da dama musamman matasa, samun damar amfani da Intanet.
“Ƙarin farashin data ba wai kawai yana hana mutane shiga Intanet ba ne, har ma yana wahalar da matasa ’yan kasuwa da masu aiki daga gida,” in ji Sanata Ekpenyong.
Shugaban majalisar, Sanata Godswill Akpabio, ya jaddada cewa samun Intanet mai arha zai taimaka wa ƙananan ’yan kasuwa da tattalin arziƙin ƙasa gaba ɗaya.
Majalisar ta buƙaci gwamnati da ta tsara manufofi da za su tabbatar da farashi mai sauƙi, tare da kafa cibiyoyin fasaha masu rangwame ga ɗalibai, ’yan kasuwa, da masu aiki da fasahar zamani.
Haka kuma, ta umarci Kwamitin Sadarwa na majalisa da ya binciki dalilan tashin farashin data tare da nemo mafita mai ɗorewa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Farashin Data Majalisar Dattawa Rage Kuɗin Data Sadarwa
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnati Ta Yi Karin Haske Kan Biyan Tallafin Rage Radadi Da Mafi Karancin Albashi
Da yake maida martani, Mokwa ya ce gwamanti ta fara biyan bashin tallafin rage radadin ga ma’aikata. Ya ce za a ci gaba da biyan kudin ne kashi-kashi har zuwa nan da watanni hudu masu zuwa.
“Mun fara biyan bashin nira 35,000 ga ma’aikata. Illar kawai wasu ma’aikatu da suka kasance masu cin kashin kansu da suke biyan tallafin kai tsaye, misali, hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa.
“Amincewa da tallafin naira 35,000 ga ma’aikata shi ne mafita ta wucin gadi da gwamnatin tarayya ta yi kafin amincewa da mafi karancin albashi na naira 70,000.
“Wannan ya faru a cikin watanni biyar, amma kungiyar kwadago ta ce ba a fara biya a kan lokaci ba, yanzu kenan akwai bashin watanni biyar.
“A cikin tallafin na watanni biyar, mun biya na wata guda. Yanzu haka tallafin watanni hudu ne suka rage, kuma za a biya su daki-daki,” ya shaida.
Kazalika, Mokwa ya fayyace zare da abawa da cewar gwamnatin tarayya ta fara biyan albashi mafi karanci ga dukkanin ma’aikatu, rassa da sashi-sashi na gwamnatin tarayya.
“Dangane da biyan albashi mafi karanci kuwa, an aiwatar da shi ga dukkanin ma’aikatu,” ya kara tabbatarwa.
Idan za a tuna dai a watan Yuli ne Shugaban kasa Tinubu ya sanya hannu kan dokar mafi karancin albashi.
Sai dai, duk da amincewa da mafi karancin albashi, har yanzu akwai korafe-korafe kan cikakken aiwatar da shi daga jihohi da kuma tarayya baki daya kusan shekara guda kenan.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp