A wani ɓangare na bikin Ranar Yaƙi da Cin Hanci ta Afirka, Shugaban

Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa (EFCC), Mr. Ola Olukoyede, ya yi gargaɗi kan barazanar da ke ƙara ƙamari na damfara ta hanyar kuɗaɗen zamani da kuma zuba jari na bogi a Najeriya da sauran sassan nahiyar.

 

Mr. Olukoyede ya bayyana hakan ne a yayin bukin ranar yaƙi da cin hanci da rashawa ta Afirka a wajen wani taron tattaunawa da aka gudanar a ofishin EFCC na shiyyar Kaduna.

 

Darakta na riko na shiyyar Kaduna, Bawa Usman Kaltungo wadda ya wakilici Shugaban EFCC ya bayyana cewa nahiyar Afirka na ci gaba da fama da mummunar illar cin hanci da rashawa, musamman ta hanyar fitar da kuɗaɗen haram zuwa ƙasashen waje, wanda ya ce ya zama babban cikas ga ci gaban ƙasashen nahiyar.

 

A cewarsa, Afirka na asarar biliyoyin daloli duk shekara ta hanyar waɗannan haramtattun kudade, inda wanke kuɗi ke zama mafi yawa a cikin irin waɗannan laifuka.

 

Sai dai kuma, Mr. Olukoyede ya jaddada cewa wata sabuwar barazana da ke ƙara yawaita ita ce damfara ta hanyar kuɗaɗen zamani da na’ura, kamar su cryptocurrencies da digital tokens.

 

“Kuɗaɗen zamani da kansu ba laifi ba ne,” in ji shi. “Amma amfani da su ta hanyar yaudara ko rashin bin doka shi ke mayar da su kayan aikata laifi. Abin takaici, masu laifi sun fara amfani da wannan fasaha wajen ɓoye kuɗaɗen sata, kaucewa bincike, da kuma aiwatar da shirye-shiryen zuba jari na bogi.”

 

Shugaban EFCC ya ce akwai ’yan siyasa da suka fara ɓoye dukiyar da suka sata ta hanyar cryptocurrency don kaucewa kamun hukumar. A cewarsa, digital wallets na amfani wajen adana kuɗaɗen da ba a iya bayyana asali, kuma ana amfani da fasahar blockchain wajen biyan kuɗin ayyuka marasa tushe.

 

Sai dai ya jaddada cewa EFCC ta samu ci gaba mai ma’ana wajen bankado da gurfanar da masu aikata irin waɗannan laifuka, inda ya ambaci nasarar da aka samu a bincike da gurfanar da shari’ar damfara ta CBEX.

 

“Damfara ta kuɗaɗen zamani da zuba jari ba sabbin ƙalubale ba ne ga EFCC,” in ji shi. “Ta hanyar amfani da basira da horarwa, muna samun nasarori a aikace.”

 

Ya kuma bayyana damuwa kan yadda damfara ta hanyar zuba jari kamar Ponzi scheme ke yaduwa a fadin Afirka, yana mai cewa masu yaudara na amfani da halin tsananin bukata da rashin sani na masu zuba jari don damfararsu.

 

Ya ce duk wata hanyar amfani da mutane da nufin amfana da su ta yaudara laifi ce, duk da irin tsarin da aka ɗaura mata.

 

Mr. Olukoyede ya yi kira ga jama’a da su guji yanke shawarar zuba jari ba tare da bincike da tabbaci ba, yana mai cewa mafi yawan mutanen da ake damfarawa su ne waɗanda ba sa kai rahoton ababen da ke da alamun damfara har sai da suka rasa kuɗaɗensu.

 

“Babu wata damfara ta zuba jari da za ta yi nasara ba tare da sakacin masu zuba jari ba,” in ji shi. “Ya zama wajibi a waye kai, a nemi sani, kuma a dauki matakan kariya tun da wuri.”

 

Ya sake jaddada cewa EFCC za ta ci gaba da haɗin gwiwa da dukkan masu ruwa da tsaki don hana da kuma binciken irin waɗannan laifuka, yana mai cewa faɗakarwa da wayar da kai na da muhimmanci matuƙa.

 

“Akwai buƙatar ilimi da fahimta,” ya ƙara da cewa. “Wannan dandalin tattaunawa wata dama ce ta musayar ra’ayi da fitar da hanyoyin warware wannan matsala. Masana su bayyana wa mahalarta ainihin yadda kuɗaɗen zamani ke aiki, don a rufe kofar da masu damfara ke amfani da ita.”

 

A ƙarshe, Mista Olukoyede ya buƙaci mahalarta taron da su yi magana cikin gaskiya da faɗakarwa, yana fatan taron zai haifar da fahimta mai zurfi da matakan haɗin gwiwa wajen yaƙi da wannan barazana.

COV: Adamu Yusuf

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Damfara Gargadi Hanyar Jari Kuɗaɗen

এছাড়াও পড়ুন:

Dan Majalisar Jema’a/Sanga, Daniel Amos, Ya Koma Jam’iyyar APC

Harkokin siyasa na Kudancin Kaduna ya dauki wani salo yayin da dan majalisar da ke wakiltar mazabar Jema’a/Sanga a majalisar tarayya, Hon. Dan Amos, ya sanar da komawarsa jam’iyyar APC mai mulki zuwa jam’iyyar PDP,  yana mai cewa ya dauki wannan mataki ne domin ya hada kai da gwamnatocin jiha da na tarayya don cigaban yankin.

Yayin da yake jawabi ga manema labarai a Kafanchan kafin karbar sa a hukumance tare da Sanata Marshall Katung, Amos ya bayyana cewa wannan mataki ya biyo bayan dogon shawarwari da aka yi da shugabannin al’umma, kungiyoyin addini, kwararru da kuma sarakunan gargajiya a fadin mazabarsa.

Ya ce jam’iyyar PDP, wacce a da take da karfi sosai a Kaduna, ta ragu saboda rikice-rikicen cikin gida da suka dade suna faruwa, wanda hakan ya janyo ficewar mambobi da kuma rasa goyon bayan talakawa a fadin kasa.

“Mun dauki lokaci muna tattaunawa da mutane a matakai daban-daban – daga tsarin jam’iyya zuwa kungiyoyin addini da na kwararru – kuma abin da muka cimma shine, don amfanin jama’armu, ya dace mu nemi wata madogara ta daban,”

“Ya zama sauki mu shiga APC saboda muna ganin irin kokarin da Shugaba Bola Ahmed Tinubu da Gwamna Uba Sani ke yi wajen hada yankin Kudancin Kaduna cikin shirin cigaba da ci gaba da kasa.” in ji Amos.

Dan majalisar ya yaba wa Shugaba Tinubu bisa nadin ɗan asalin yankin, Janar Christopher Musa, a matsayin Babban Hafsan Tsaro (CDS) da kuma amincewa da a kafa Jami’ar Kimiyyar Aiki ta Tarayya da Asibitin Tarayya (Federal Medical Centre) a yankin.

Ya kuma gode wa Gwamna Uba Sani saboda gudanar da mulki cikin hadin kai, gina ababen more rayuwa, da bude kofa ga kowa, wanda ya ce ya karfafa zumunci da bai wa kowane bangare na jihar damar shiga.

“Shugaban kasa da gwamna suna nuna shugabanci na hada kan jama’a. Wannan ya sa muka ga dacewar mu hade da su domin mu samu karin cigaba a yankinmu,” in ji Amos.

Amos ya karyata jita-jitar cewa ya koma APC don son kai ko muradin siyasa, yana mai cewa wannan mataki ne na Allah da kuma na amfanin jama’ar Kudancin Kaduna.

“Ba don bukatar kaina ba ne, amma don mu tabbatar da yankinmu ya ci gajiyar dimokuradiyya. Ina da yakinin cewa tarihi zai tuna da mu bisa wannan mataki na jarumta da muka dauka,” ya kara da cewa.

Dan majalisar, wanda shi ne Shugaban Kwamitin Ayyukan Majalisa, ya tabbatar wa mazaunar mazabarsa cewa komawarsa APC ba za ta canza manufarsa ta kyakkyawan wakilci ba, yana mai cewa ya shiga jam’iyyar mai mulki ne don kara daraja, ba don kawo rarrabuwar kawuna ba.

Ya bayyana fatan cewa da hadin kai tsakanin jama’a da gwamnati, Kudancin Kaduna zai ci gaba da samun cigaba a bangaren ababen more rayuwa, ilimi, da tsaro.

An shirya taron karbar Amos, Sanata Katung, da sauran wadanda suka koma daga PDP zuwa APC a ranar 1 ga Nuwamba a Kafanchan, kuma manyan baki da ake sa ran halarta sun hada da Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima, Kakakin Majalisar Wakilai, Rt. Hon. Tajudeen Abbas, da kuma shugabannin jam’iyyar APC daga fadin kasar nan.

Radio Nigeria ta ruwaito cewa wannan sauyin jam’iyya ya nuna babban sauyi a siyasar jihar Kaduna, wanda ya kawo karshen rinjayen PDP da ta yi sama da shekaru 25 a Kudancin jihar.

Daniel Karlmax

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu zai gana da Trump kan zargin kisan Kiristoci a Nijeriya 
  • Iran Ta Gargadi Isra’ila Kuma Tasha Alwashin Kare Shirinta Na Nukiliya
  • Dan Majalisar Jema’a/Sanga, Daniel Amos, Ya Koma Jam’iyyar APC
  • Jerin Gwarazan Taurarinmu
  • Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa
  • Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC
  • M D Duniya Tayi Gargadi Game Da Gwajin Nukiliya Da Amurka Ta Sanar Za ta yi
  • Gwamnatin Yobe ta ƙaddamar da shirin amfani da ma’adanai
  • Manoma a Jigawa Sun Jinjinwa Kungiyar Sasakawa Africa Bisa Bada Tallafi a Harkar Noma
  • Ƙungiyar Rays Heaven ta Ƙarfafa Wayar da Kai kan Lafiyar Kwakwalwa a Kaduna