Shugaban Yahudawan Iran Ya Tuhumi Isra’ila Da Fakewa A Karkashin Addini
Published: 10th, July 2025 GMT
Shugaban yahudawan Iran Rabbi Younes Hamami Lalezar ya ce, Isra’ila tana amfani da addini yahudanci domin cimma manufofinta, tana kuma bayyana Iran a matsayin wacce take fada da addinin yahudanci,alhali a cikin iran da akwai zaman lafiya tsakanin Mabiya dukkanin addinai.
Haka nan kuma ya ce, kiyayyar da Isra’ila take da shi akan Iran ne, yake sa take jinginawa Iran din kin jinin yahduawa,wanda aikin ‘yan sahayoniya ne su samar da rabuwar kawuna a tsakanin al’ummar Iran bisa addini da kuma kabila.
Isra’ila tana bayyana kanta a matsayin mai bai wa yahudawa kariya, sai dai da dama daga cikin Mabiya addinin yahudanci, wadanda ba ‘yan sahayoniya ba, suna zarginta da amfani da addini saboda manufofi na siyasa.
Fiye da shekaru 2,700, yahudawa suke rayuwa a cikin Iran,kuma suna da wuraren bautarsu da harkokinsu na yau da kullum ba tare da tsangwama ba.
Rabbi Younes Hamami Lalezar ya kuma ce: A Iran, yahudawa suna aiki, suna yin bautarsu, da rayuwa a ko’ina, suna da dakunansu na ibada -Synagogues- a cikin sauki da ‘yanci ba tare da wata kariya ta jami’an tsaro kamar yadda yake a cikin kasashen turai ba.
Haka nan kuma ya ce, yadda muke rayuwa ta girmama juna a tsakanin musulmi, yahudawa, da kiristoci, shi ne babban abinda yake bayyana hakikaninmu, don haka duk wani zargi na kin jinin yahudawa ba shi da madogara.”
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Dangote Ya Yaba Wa Tinubu Kan Samar Da Ababen More Rayuwa A Nijeriya
Wannan sabon birni na da ganuwa mai tsawon kilomita 8.5 da zai kare Legas daga ambaliyar ruwa, kuma yana da gidaje, ofisoshi da wuraren kasuwanci da na nishaɗi.
Dangote ya ce wannan aiki yana daga cikin manyan abubuwan tarihin da Shugaba Tinubu zai bari.
Hakazalika, ya nuna godiyarsa bisa fara aikin titin gaɓar teku daga Legas zuwa Kalaba da kuma aikin titin Sakkwato zuwa Badagry, waɗanda za su inganta sufuri da tattalin arziƙi a faɗin ƙasar.
Ya kwatanta hangen nesan Tinubu da yadda ƙasar Netherlands ta kasance wajen samar da muhallai a cikin ruwa don raya birane.
Dangote ya ƙara da cewa kamfaninsa na jin daɗin irin goyon bayan da gwamnati ke ba shi wajen sauƙaƙa kasuwanci da bunƙasa tattalin arziƙi.
Ya ce Nijeriya na fuskantar barazanar ambaliya, wanda hakan ya sa gidauniyarsa ta Aliko Dangote Foundation ke shirin ƙaddamar da wani Asusun Tallafa wa Matsalar Sauyin Yanayi domin taimaka wa al’ummar da ambaliya ke shafa a faɗin ƙasar.
Dangote ya roƙi Allah Ya bai wa Shugaba Tinubu hikima da nasara wajen jagorantar Nijeriya, sannan ya tabbatar masa da goyon bayan kamfaninsa da dukkanin ‘yan kasuwa masu kishin ci gaban ƙasa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp