Kwastam ta kama mazaƙutar jakai da aka yi yunƙurin safararsu
Published: 10th, July 2025 GMT
Hukumar hana fasa ƙwauri ta Najeriya (Kwastam), ta ce ta kama wata mota da ke ɗauke da wata kontena maƙare da mazaƙutar jakai a kan hanyar Kaduna zuwa Abuja.
Hukumar ta Kwastam ta sanar da kama motar ne a ranar Alhamis.
Sojoji sun tarwatsa matsugunin ’yan ta’adda da kashe wasu a Borno An gurfanar da wasu kan zargin kashe matafiya bikin aure a JosAn gano waɗanda suka yi safarar ne da ake zargin suna shirin fitar da shi zuwa ƙasashen waje ba bisa ƙa’ida ba.
An samu nasarar ne a ranar Juma’a 5 ga watan Yuni, 2025, da misalin ƙarfe 9 na dare, bayan wani haɗin gwiwa da jami’an ofishin kula da namun daji na musamman da na hukumar Kwastam suka gudanar.
Kwaturola Janar na Hukumar kwastam, Mista Adewale Adeniyi ne ya bayyana hakan a wani taron manema labarai a Abuja ranar Alhamis.
Maimagana da yawun hukumar ta Kwastam, Abdullahi Aliyu Maiwada wanda ya wakilci Kwanturola Janar na Kwastam ya bayyana cewa, nasarar kama masu aikata hakan na cikin ƙoƙarin da ake yi na daƙile kasuwancin dabbobin dawa ta ɓarauniyar hanya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Hukumar Kwastam
এছাড়াও পড়ুন:
ADC: Tinubu Na Yunƙurin Raba Kawunan Masu Haɗaka Kafin Zaɓen 2027
ADC ta tunatar da Tinubu cewa da gwamnatin Goodluck Jonathan ba ta jure hamayya ba a baya ba, shi ma ba zai kai matsayin shugaban ƙasa ba, kuma APC ba za ta lashe zaɓe ba.
Jam’iyyar ta ce ya kamata shugaban ƙasa ya nuna cewa yana goyon bayan gaskiya da ‘yancin jam’iyyu a tsarin dimokuraɗiyya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp