Cikin adadin, masu bayyana ra’ayoyi daga kasashen Saudiyya da Serbia, suna cikin mafiya bayyana matukar baiken matakin na Amurka, da karin kaso 28.5 bisa dari. Yayin da a daya bangaren al’ummun Malaysia, da Isra’ila, da Australia, da Singapore, da Philippines, da Najeriya, da Portugal, da Pakistan, da Afirka ta kudu, kasonsu na nuna baiken matakan kara harajin na Amurka ya karu da sama da kaso 20 bisa dari.

(Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Hukumar Kula da Muhalli ta Jihar Jigawa ta Kwace Gurbatattun Kayayyaki na Miliyoyin Naira

Hukumar Kula da Muhalli ta Jihar Jigawa (JISEPA) ta yi kira ga al’umma da su ba da hadin kai wajen tabbatar da tsafta da kuma bayar da rahoton duk wani da ake sayarwa da ba bisa ka’ida ba, ko kuma cikin rashin tsafta.

Babban Daraktan Hukumar, Alhaji Adamu Sabo ne ya bayyana hakan yayin taron manema labarai da aka gudanar a Dutse, babban birnin jihar Jigawa.

A cewarsa, wannan kira ya zama wajibi sakamakon nasarar da hukumar ta samu na kwace gurbatattun kayayyakin na sama da naira miliyan 14 a lokacin sintiri da binciken kayayyaki a fadin jihar daga watan Janairu zuwa Yuni na shekarar 2025.

Alhaji Adamu Sabo ya kara da cewa, mafi yawancin kayayyakin da aka kwace na ci ne da suka lalace, ko kuma wadanda aka adana ba bisa ka’ida ba, ko kuma suka lalace har suna barazana ga muhalli da lafiyar jama’a.

Ya bayyana cewa wann

an sintiri na tabbatar da tsafta yana cikin ayyukan hukumar domin inganta lafiyar jama’a da tabbatar da tsaron muhalli, tare da tabbatar da ka’idojin tsafta.

Sabo ya ce dukkan kayayyakin da aka kama an kaddamar da su bayan an bi dukkan matakan doka, an tantance su, sannan aka amince da lalata su bisa dokokin kiwon lafiya na jama’a.

“Wannan aikin an gudanar da shi ne bisa tsarin doka kamar yadda sashe na 5(1)(2) na Dokar Kariya ta Muhalli ta Jihar Jigawa ta shekarar 2009 (wanda aka gyara), da kuma sashe na 125(1) na Dokar Tsaron Lafiyar Jama’a ta Jihar Jigawa ta shekarar 2024 suka tanada”. In ji shi.

Ya jaddada cewa, wannan mataki  rigakafi ne na kare lafiyar jama’a da tabbatar da tsaron muhalli da tsaftar Jihar Jigawa ba don kuntatawa wani ba.

Ya kara da cewa, hukumar za ta ci gaba da yin aiki tare da kungiyoyin kasuwa, ‘yan kasuwa da shugabannin al’umma domin tabbatar da cikakken bin dokokin muhalli da na lafiyar jama’a.

 

Usman Muhammad Zaria

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin Ta Kafa Kungiyar Masana Masu Binciken Sararin Samaniya Mai Zurfi Ta Farko
  • Asibiti Mai Zaman Kansa A Kano Zai Fara Aikin Manyan Tiyatu Tare Da Rage Kuɗi Kaso 50%
  • Asibiti Mai Zaman Kansa A Kano Zai Fara Manya Manyan Tiyatu Tare Da Rage Kuɗi Kaso 50%
  • China Ta Mayar Da Martani Kan Barazanar Trump Na Ƙarin Haraji Ga Kasashen BRICS
  • Hukumar Kula da Muhalli ta Jihar Jigawa ta Kwace Gurbatattun Kayayyaki na Miliyoyin Naira
  • Trump Ya Yi Barazanar Ƙarin Haraji Ga Ƙasashen Da Suka Rungumi BRICS
  • Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin
  • Wang Yi: Amfani Da Karfin Soji Ba Bisa Ka’ida Ba Na Ingiza Karuwar Tashin Hankali
  • Ku Manta Da 2027, Tinubu Zai Ci Gaba Da Mulki Har 2031 — Fadar Shugaban Ƙasa Ga ADC
  • Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN Ta Nuna Goyon Baya Ga Fadadar Kungiyar BRICS A Matsayin Hanyar Bunkasa Hadin Gwiwa