Leadership News Hausa:
2025-11-13@18:38:59 GMT

Yanayin Rudani Na Tsawon Kwanaki 100 Kashedi Ne Ga Amurka

Published: 30th, April 2025 GMT

Yanayin Rudani Na Tsawon Kwanaki 100 Kashedi Ne Ga Amurka

A ganin gwamnatin Amurka, manufar ramuwar haraji za ta taimaka wajen farfado da masana’antu a kasar da kara samar da guraben aikin yi, amma yadda ta daidaita matsalolin tattalin arzikinta ba ta hanyar da ta dace ba, da kuma gazawa wajen bin ka’idojin tattalin arziki, ya haifar da damuwa a zukatan al’umma da kuma tsoro a kasuwanni, lamarin da ya sa Amurka ta kara shiga mawuyacin hali.

 

Cikin kwanaki 100 da suka shude, wasu kasashen duniya sun ki mika wuya ga cin zalin Amurka ta fuskar manufar ramuwar haraji. Misali, kasar Sin ta fara mayar da martani, a kokarin kiyaye halastattun hakkokinta da tsarin tattalin arziki da cinikayya da ma na adalci a duniya. Kana kuma kungiyar tarayyar Turai EU ta zartas da matakan mayar da martani kan Amurka a zagaye na farko. Firaministan kasar Japan Ishiba Shigeru kuma ya bayyana a fili cewa, bai shirya mika wuya don cimma yarjejeniya kan harajin kwastam cikin hanzari ba.

 

Yanayin rudani da Amurka ke ciki cikin kwanaki 100 da suka gabata ya ilmantar da jama’a cewa, babu wanda zai yi danniya bisa ganin dama. Kuma babu wanda zai hana dunkulewar tattalin arzikin duniya. Hadin gwiwa mai kunshe da kowa da samun moriyar juna da nasara ga ko wane bangare, ita ce hanyar da ta dace. (Tasallah Yuan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Namadi Ya Kaddamar Da Aikin Gina Hanyoyi Ba Naira Biliyan 81 A Malam Madori

Daga Usman Muhammad Zaria

 

Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya jaddada kudirin gwamnatin sa na ci gaba da bunkasa hanyoyin sufuri a fadin jihar.

Gwamnan ya bayyana hakan ne yayin da ya kaddamar da wani muhimmin aikin gina hanyoyi a karamar hukumar Mallam Madori.

Yayin taron kaddamarwar, Gwamna Namadi ya bayyana cewa aikin yana cikin shirin “Gwamnati da Jama’a” wanda ke karfafa al’umma, rage matsalolin sufuri da kuma karfafa harkokin kasuwanci.

Ya ce shirin ya kunshi gina manyan hanyoyi guda shida a sassan jihar, masu tsawon kilomita 179 gaba daya, a kan kudin da ya haura Naira Biliyan 81.

Hanyoyin sun hada da Mallam Madori zuwa Gari Uku zuwa Kanya Babba zuwa Malorin Kasim, ta ratsa ta Abori Sumburtu, har zuwa Diginsa, mai tsawon kilomita talatin da hudu da rabi.

Sai kuma hanyar Arbus zuwa Girbobo zuwa Garin Bukar mai nisan kilomita talatin da uku da rabi.

Kazalika akwai hanyar Dundubus zuwa Yanjaji zuwa Wangara mai tsawon kimanin kilomita goma sha bakwai.

Akwai kuma hanyar Jahun zuwa Takalafiya zuwa Zareku zuwa Kafin Hausa da reshe daga Takalafiya zuwa Dangyatum mai kilomita talatin da takwas.

Da hanyar Kukayasku zuwa Malamaba zuwa Katuka zuwa Garin Kwalandi mai nisan kilomita talatin da hudu da rabi.

Sai cikon ta shidda wacce ta tashi daga Farun Daba zuwa Maitsani zuwa Baauzini zuwa Kafin Chiroma zuwa Gallu Babba zuwa Gallu Karama ta kai ga Karkarna Bypass mai nisan kilomita goma sha uku.

Gwamnan ya bayyana cewa tuni an yi kashi 35 cikin 100 aikin,  yana mai fatan cewa za a gama shi cikin shekara guda, kafin wa’adin watanni 18.

Ya tabbatar da cewa gwamnatin sa za ta ci gaba da baiwa ababen more rayuwa, ilimi, kiwon lafiya, noma da samar da ayyukan yi muhimmanci a karkashin Manufofi 12 na Gwamnati don Cigaban Jigawa.

Ya kuma gode wa Gwamnatin Tarayya a karkashin Shugaba Bola Ahmed Tinubu bisa tallafi da daidaiton manufofi.

A yayin ziyarar, Gwamna Namadi ya kuma kaddamar da sabon masallaci da aka gina a Garin Gabas, wanda shugaban karamar hukuma ya tallafa wajen ginawa.

Shugabannin al’umma sun mika wa Gwamnan kundin bukatun jama’a a matsayin wani bangare na tsarin mulkin jin ra’ayin al’umma.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Babu Wani Abu Kuskure Ga Sojan Da Ya Yi Sa-in-sa Da Ministan FCT – Matawalle
  • Sin Ta Mayar Da Martani Game Da Matakin Amurka Na Dakatar Da Ka’idar Fadada Jerin Wadanda Kasar Ta Takaita Fitar Wa Kayayyaki
  • Sin Ta Yi Kira Da A Inganta Mika Mulki Cikin Kwanciyar Hankali A Sudan Ta Kudu
  • MDD ta sanya Najeriya cikin ƙasashe 16 da ke fama da tsananin yunwa
  • Sin: Amurka Ba Ta Sa Lura Ga Kare Hakkin Dan Adam
  • Babu wani gwamna da zai yi ƙorafin ƙarancin kuɗi a mulkin Tinubu — Sanwo Olu
  • CIIE Ya Kasance Gadar Sada Tattalin Arzikin Kasar Sin Da Na Duniya
  • An buƙaci tsige shugaban APC na Kuros Riba
  • Larijani : ‘babu wani sabon sako’ da muka aika wa Amurka
  • Gwamna Namadi Ya Kaddamar Da Aikin Gina Hanyoyi Ba Naira Biliyan 81 A Malam Madori