An kama mutum 3 kan zargin sata da ƙone gidan bature a Gombe
Published: 27th, March 2025 GMT
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Gombe, ta kama wasu mutum uku da ake zargi da laifin sata da kuma ƙone gidan wani Bature a unguwar G.R.A, kusa da gidajen ’yan majalisa a jihar.
Waɗanda aka kama sun haɗa da Hannatu Ibrahim mai shekaru 28 daga Kumo, Ahmed Adamu mai shekaru 20, da Abubakar Ibrahim mai shekaru 28.
A cewar kakakin rundunar, DSP Buhari Abdullahi, lamarin ya faru ne ranar 22 ga watan Maris, 2025 da misalin ƙarfe 8 na dare.
Sanarwar ta bayyana cewa Hannatu Ibrahim, wacce ke aiki a matsayin mai girki ga Mohammed Jurdi, wanda ɗan kasar Siriya da ke aiki da kamfanin Triacta Nigeria Limited, ta sace dala 35,000 (kimanin Naira miliyan 53.5) tare da banka wa gidan wuta.
Bayan samun rahoton, ‘yan sanda sun garzaya wajen, inda suka kama ta tare da gano dala 7,100 a wajenta.
A yayin bincike, ta ce Ahmed Adamu ne, mutum na farko da ta tuntuɓa bayan aikata laifin.
An samu dala 100 a cikin sakar hannunsu.
An kuma kama Abubakar Ibrahim, mai gadin gidan da aka yi satar, wanda ake zargi da taimaka musu wajen aikata laifin.
DSP Abdullahi, ya ce suna ci gaba da bincike, kuma suna shirin gurfanar da waɗanda ake zargi a gaban kotu.
Ya kuma tabbatar wa jama’a cewa rundunar za ta ci gaba da yaƙi da laifuka tare da tabbatar da adalci a jihar.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Jiragen Yakin Amurka Sun Kashe Mutane Da Dama A lardin Sa’ada Na Kasar Yemen
Mutane da dama daga nahiyar Afirka ne suke cikin mutane kimani 50 wadanda suka rasa rayukansu sanadiyyar hare-haren da jiragen yakin Amurka suka kai kan wani gidan kaso a lardin Sa’ada na kasar Yemen.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto kamfanin dillancin labaran Al-Masirah yana cewa makaman Amurka sun fada kan wani gidan yarin da aka kebewa yan Afrika, kuma yawansu ya kai 115, amma har yanzun ba’a san yawan wadanda suka rasa rayukansu a gidan yari.
Labarin ya kara da cewa har yanzun ma’aikatan agaji suna aikin ceto a wurin, sannan hotunan da suka fara bayyana sun nuna gawaki da dama. Amma Al-Masirah ta bayyana cewa akalla mutane 68 sun rasa rayukansu.