Kamfanin Hisense South Africa, da kamfanin CNBM, sun sanya hannu kan wata yarjejeniyar hadin gwiwa bisa matsayin koli, ta gudanar da aikin samar da hidimomin kyautata amfani da makamashi mai tsafta a Afirka ta kudu.

Kamfanonin biyu sun rattaba hannu kan yarjejeniyar ne a jiya Talata, a birnin Johannesburg, yayin bikin baje hajojin da suka shafi sabbin makamashi, daya daga baje koli mafi girma da ake gudanarwa a nahiyar Afirka a fannin makamashi mai tsafta, wanda ke gudana yanzu haka a birnin.

Bayan sanya hannu kan yarjejeniyar, babbar manajan sashen lura da hadin gwiwar kamfanin CNBM a kasashen ketare Jiang Fei, ta shaidawa kamfanin dillancin labarai na kasar Sin Xinhua cewa, sabon hadin gwiwar zai taimakawa Afirka ta kudu, da ikon cin gajiyar isasshen makamashi.

Jiang Fei ta kara da cewa, kamfanin Hisense South Africa da CNBM, za su samarwa ‘yan kasar mitoci irin na zamani, da wuraren caji, da ma’ajiyar makamashi da sauran hidimomi na zamani, wadanda za su baiwa Afirka ta kudu damar sauya alaka zuwa amfani da makamashi mai tsafta. (Mai fassara: Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Tarayyar Afirka ta dage takunkumin da ta kakabawa Gabon

Kungiyar Tarayyar Afirka ta dage takunkumin da ta kakabawa kasar Gabon tare da maida ta a cikin cibiyoyinta.

AU, ta sanar da hakan ne yayin taron kwamitin zaman lafiya da tsaro na kungiyar yau Laraba a Addis Ababa.

Hakan dai ya karshen dakatarwar da aka yi wa kasar ta Gaban daga kungiyar, watanni 20 bayan juyin mulkin da sojoji suka yi a watan Agustan 2023.

Kwamitin zaman lafiya da tsaro na AU, ya yi la’akari da mika mulki da ya hambarar da Ali Bongo “gaba daya cikin nasara,” saboda haka ya yanke shawarar dage takunkumin nan take.

‘’Tsarin siyasar Gabon yana da ” gamsarwa” inji sanarwar kungiyar.

Wannan matakin na AU ya zo ne kwanaki uku gabanin rantsar da Janar Brice Oligui Nguema, wanda aka zaba a matsayin shugaban kasar a ranar 12 ga Afrilu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • AU ta janye takunkumin da ta ƙaƙaba wa Gabon
  • Iran ta sha alwashin ci gaba da aiwatar da manufofinta na raya dangantakarta da Nijar
  • Tarayyar Afirka ta dage takunkumin da ta kakabawa Gabon
  • Amurka ta sake laftawa wasu kamfaninin mai na Iran takunkumi
  • Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci Na Iran Ya Ce: Maganar ‘Yan Sahayoniyya Rudu Ne Maras Amfani
  • Abubuwan Da Na Gani A Yankin ‘Hero Bay’ Da Ke Cikin Kasar China
  • HKI Tana Amfani Yunwa A Matsayin Makamin Yaki  A Kan Falasdinawa A Gaza
  • Sin Za Ta Aiwatar Da Matakan Daidaita Samar Da Guraben Ayyukan Yi Da Raya Tattalin Arziki
  • Gwamnatin Tarayya Ta Umurci WAEC, NECO Su Koma Amfani Da CBT Nan Da 2026
  • Ma’aikata 240 na karɓar albashi biyu, wasu 217 na amfani da lambar BVN ɗaya a Kano