Aminiya:
2025-09-17@22:14:09 GMT

Sojoji sun tarwatsa matsugunin ’yan ta’adda da kashe wasu a Borno

Published: 10th, July 2025 GMT

Dakarun sojojin Nijeriya na rundunar sojojin sama tare da haɗin gwiwar Operation Haɗin Kai sun kai farmaki kan wasu muhimman wuraren da ’yan ta’adda suka mamaye a tsaunin Mandara da ke Jihar Borno.

An samu labarin cewa rundunar sojin sama ta gudanar da samamen ta ne a wani wuri da aka san shi da tudu mai tsauni, wanda ke kan iyakar Nijeriya da Kamaru, bayan samun bayanan sirri.

An gurfanar da wasu kan zargin kashe matafiya bikin aure a Jos ’Yan sanda sun ƙaddamar da sabon samame, sun kama mutum 98 a Kano

Daily Trust ta ruwaito cewa, samamen share fagen ya zo ne ƙasa da sa’o’i 24 da shugaban ƙasa, Bola Tinubu ya umurci sojoji da su kawar da duk maƙiya da ke barazana a ƙasar nan.

Kakakin rundunar sojin sama na Nijeriya, Ehimen Ejodame ya shaidawa manema labarai a Abuja cewa, aikin sa ido da binciken da sojojin ke yi ya ba da alamun cewa maharan na shirin kai hare-hare.

Air Commodore, Ejodame ya yi bayanin cewa matsugunin da suke amfani da shi mai amfani da lantarki da na’urar hasken rana da baƙaƙen tutoci, alama ce ta sake farfaɗowar maharan a wurin kafin a kai musu harin bam a tarwatsa su.

A cewarsa, manyan samamen, Wa Jahode da Loghpere, sun daɗe suna zama mafaka ga Ƙungiyar Jama’atu Ahlis Sunna Lidda’awati wal-Jihad (JAS), ɓangaren ’yan Boko Haram da ke da matsuninsu a can.

Ya ce, baya ga yadda aka tarwatsa matsunin ta sama da ya lalata kayan aikin ‘yan ta’addar, an kashe da dama daga cikinsu ciki har da kwamandojin su a harin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: tsaunin Mandara

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan ‘Mafiya’ na ƙoƙarin kashe matatar man fetur da na gina —Ɗangote

Mai kuɗin Afrika kuma Shugaban Matatar Mai ta Ɗangote, Alhaji Aliko Ɗangote, ya zargi wasu manyan masu harkar mai da shirya maƙarƙashiya domin kashe matatarsa.

Ɗangote ya yi zargin cewa miyagun ’yan kasuwan suna ƙoƙarin kashe matatar mansa mai darajar dala biliyan 20, kamar yadda aka kashe masana’antar tufafi ta ƙasar.

Ya bayyana haka ne a ranar Litinin a Legas yayin bikin cika shekara ɗaya da fara samar da fetur a matatar, inda ya ce tafiyar ta kasance cike da ƙalubale tun daga farko.

“A gaskiya tafiyar shekara ɗaya da ta wuce ta yi mana matuƙar wuya. Mun zo mu sauya tsarin kasuwancin man ƙasa. Amma wasu na ganin mun raba su da hanayar cin abinci bakinsu,” in ji shi.

’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu NAJERIYA A YAU: Matsayin Doka Kan Hawa Mumbari Ba Tare Da Izinin Gwamnati Ba

Ya ci gaba da cewa, “Amma abin da muka yi shi ne mun sa Najeriya da nahiyar Afirka gaba ɗaya su yi alfahari.”

Ɗangote ya ce matatar ta riga ta fitar da lita biliyan 1.8 na man fetur zuwa ƙasashen waje cikin watanni uku da suka gabata, sannan tana da isasshen ƙarfi wajen cika buƙatar cikin gida.

Ya ce tun daga fara aikin matatar a watan Satumbar 2024, dogayen layukan man fetur da suka fi shekaru 50 ana fama da su a Najeriya sun zama tarihi.

Ɗangote ya ƙara da cewa farashin fetur ya sauka daga kusan Naira 1,100 zuwa N841 a wasu jihohi, kuma da zarar sabbin motocin gas (CNG) masu dakon mai sun fara aiki a duk faɗin ƙasar, rage farashin zai fi tasiri.

Ya kuma bayyana cewa sabbin motocin CNG 4,000 za su samar da aƙalla ayyukan yi 24,000, ciki har da direbobi, makanikai da sauran ma’aikata.

“Ba mu kore kowa daga aiki ba, sai dai muna ƙara samar da ayyuka,” in ji shi.

Ɗangote ya zargi masu harkar mai da haɗa kai da ’yan kasuwa na cikin gida da na waje da ƙoƙarin hana nasarar matatar.

“Yadda aka hallaka masana’antar yadi, haka suke ƙoƙarin kashe matatar mu,” in ji shi.

A kan zargin cewa bai wadatar da ƙasa da fetur ba, sai ya mayar da martani da cewa: “Idan ba mu da ƙarfin samar da mai, me ya sa muke fitarwa zuwa ƙasashen waje?”

Ya kuma yi ba’a ga Ƙungiyar Ma’aikatan Mai (NUPENG) wadda ta ce rage farashin fetur na matatar Dangote “kyautar Girka ce.” Dangote ya ce: “Ko da kuwa kyautar Girka ce, ai kyauta ce, za ta kuma ci gaba da kasancewa.”

Ya jaddada cewa abin da Najeriya ke buƙata yanzu shi ne kare masana’antunta, domin ci-gaban tattalin arziki da kuma rage dogaro da shigo da kaya daga waje.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Microsoft ya ƙwace shafukan wasu kamfanoni 340 a Najeriya
  • Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa
  • Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Ta Kama Bisa Kuskuren Safarar Ƙwayoyi
  • Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno
  • Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba
  • ’Yan ‘Mafiya’ na ƙoƙarin kashe matatar man fetur da na gina —Ɗangote
  • ’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu
  • Rabin Sojojin Isra’ila da suka ji rauni a yakin Gaza na fama da ciwon damuwa