Aminiya:
2025-07-10@22:15:07 GMT

Sojoji sun tarwatsa matsugunin ’yan ta’adda da kashe wasu a Borno

Published: 10th, July 2025 GMT

Dakarun sojojin Nijeriya na rundunar sojojin sama tare da haɗin gwiwar Operation Haɗin Kai sun kai farmaki kan wasu muhimman wuraren da ’yan ta’adda suka mamaye a tsaunin Mandara da ke Jihar Borno.

An samu labarin cewa rundunar sojin sama ta gudanar da samamen ta ne a wani wuri da aka san shi da tudu mai tsauni, wanda ke kan iyakar Nijeriya da Kamaru, bayan samun bayanan sirri.

An gurfanar da wasu kan zargin kashe matafiya bikin aure a Jos ’Yan sanda sun ƙaddamar da sabon samame, sun kama mutum 98 a Kano

Daily Trust ta ruwaito cewa, samamen share fagen ya zo ne ƙasa da sa’o’i 24 da shugaban ƙasa, Bola Tinubu ya umurci sojoji da su kawar da duk maƙiya da ke barazana a ƙasar nan.

Kakakin rundunar sojin sama na Nijeriya, Ehimen Ejodame ya shaidawa manema labarai a Abuja cewa, aikin sa ido da binciken da sojojin ke yi ya ba da alamun cewa maharan na shirin kai hare-hare.

Air Commodore, Ejodame ya yi bayanin cewa matsugunin da suke amfani da shi mai amfani da lantarki da na’urar hasken rana da baƙaƙen tutoci, alama ce ta sake farfaɗowar maharan a wurin kafin a kai musu harin bam a tarwatsa su.

A cewarsa, manyan samamen, Wa Jahode da Loghpere, sun daɗe suna zama mafaka ga Ƙungiyar Jama’atu Ahlis Sunna Lidda’awati wal-Jihad (JAS), ɓangaren ’yan Boko Haram da ke da matsuninsu a can.

Ya ce, baya ga yadda aka tarwatsa matsunin ta sama da ya lalata kayan aikin ‘yan ta’addar, an kashe da dama daga cikinsu ciki har da kwamandojin su a harin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: tsaunin Mandara

এছাড়াও পড়ুন:

HKI: Sojoji 62 Ne Su Ka Halaka A Gaza A Cikin Wannan Shekara Ta 2025

 Jaridar HKI ta “Haaretz'” ta buga labarin da yake cewa: A cikin wannan shekarar ta 2025, sojojinsu da su ka halaka sun kai 62.

A cikin watannin bayan nan an sami karuwar sojojin mamayar da ‘yan gwgawarmaya suke kashewa a Gaza.

Yankin Khan Yunus dake Arewacin Gaza da HKI take riya cewa ta nike shi, sannan kuma ta kori Falasdinawa daga cikinsa, yana daga cikin wuraren da aka yi wa sojojin mamayar kwanton bauna.

Bugu da kari, har yanzu ‘yan gwgawarmayar suna ci gaba da harba makamai masu linzami daga Gaza zuwa matsugunan ‘yan share wuri zauna da suke kusa da Gaza.

A jiya ma dakarun “Sarayal-Quds” na kungiyar Jihadul-Islami ta sanar da harba makamai masu linzami zuwa  matsugunan da suke da Gaza.

Jaridar ta “Haaratz’ ta kuma ce, Fira ministan na HKI bai yi wa iyalan ko daya daga cikin iyalan sojojin da aka kashe a Gaza ta’aziyya  ba, balle ya gana da su.

Jaridar ta kuma ce, hotunan da ake nunawa na Netanyahu yana ganawa da iyalan sojoji tsoho ne ba sabo ba ne.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 24 a Arewa maso Gabashin Nijeriya
  • An kashe mutum ɗaya da ƙona gidaje sama da 100 a Taraba
  • ’Yan sanda sun ƙaddamar da sabon samame, sun kama mutum 98 a Kano
  • ’Yan sanda sun ƙaddamar da samamen “Operation Kukan Kura”, sun kama mutum 98 a Kano
  • Sojoji Sun Kai Hari Maɓoyar Boko Haram A Borno, Sun Kashe Wasu ‘Yan Ta’adda
  • HKI: Sojoji 62 Ne Su Ka Halaka A Gaza A Cikin Wannan Shekara Ta 2025
  • Sojoji Sun Kashe Ƴan Bindiga 30 A Katsina
  • Kakakin Rundunar Izzuddeen Qassam ya Bayyana Yadda Suka Yi Kofar Rago Ga Sojojin Mamayar Isra’ila
  • Falasdinawa 13 Ne Suka Yi Shahada Wasu Da Dama Suka Jikkata A Hare-Haren Sojojin Mamayar Isra’ila A Gaza