Sojoji sun tarwatsa matsugunin ’yan ta’adda da kashe wasu a Borno
Published: 10th, July 2025 GMT
Dakarun sojojin Nijeriya na rundunar sojojin sama tare da haɗin gwiwar Operation Haɗin Kai sun kai farmaki kan wasu muhimman wuraren da ’yan ta’adda suka mamaye a tsaunin Mandara da ke Jihar Borno.
An samu labarin cewa rundunar sojin sama ta gudanar da samamen ta ne a wani wuri da aka san shi da tudu mai tsauni, wanda ke kan iyakar Nijeriya da Kamaru, bayan samun bayanan sirri.
Daily Trust ta ruwaito cewa, samamen share fagen ya zo ne ƙasa da sa’o’i 24 da shugaban ƙasa, Bola Tinubu ya umurci sojoji da su kawar da duk maƙiya da ke barazana a ƙasar nan.
Kakakin rundunar sojin sama na Nijeriya, Ehimen Ejodame ya shaidawa manema labarai a Abuja cewa, aikin sa ido da binciken da sojojin ke yi ya ba da alamun cewa maharan na shirin kai hare-hare.
Air Commodore, Ejodame ya yi bayanin cewa matsugunin da suke amfani da shi mai amfani da lantarki da na’urar hasken rana da baƙaƙen tutoci, alama ce ta sake farfaɗowar maharan a wurin kafin a kai musu harin bam a tarwatsa su.
A cewarsa, manyan samamen, Wa Jahode da Loghpere, sun daɗe suna zama mafaka ga Ƙungiyar Jama’atu Ahlis Sunna Lidda’awati wal-Jihad (JAS), ɓangaren ’yan Boko Haram da ke da matsuninsu a can.
Ya ce, baya ga yadda aka tarwatsa matsunin ta sama da ya lalata kayan aikin ‘yan ta’addar, an kashe da dama daga cikinsu ciki har da kwamandojin su a harin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: tsaunin Mandara
এছাড়াও পড়ুন:
An gurfanar da wasu kan zargin kashe matafiya bikin aure a Jos
Rundunar ’yan sandan Jihar Filato a ranar Alhamis ta gurfanar da wasu mutane 22 da ake zargi da kashe matafiya bikin aure da a unguwar Mangun da ke Ƙaramar hukumar Mangu ta Jihar Filato.
An kashe mutum 13 daga cikin matafiyan, yayin da wasu da dama suka jikkata sakamakon harin da wasu da ake zargin ’yan daba ne suka kai lokacin da suke kan hanyarsu ta zuwa unguwar Qua da ke ƙaramar hukumar Qua’an Pan ta Jihar Filato.
’Yan sanda sun ƙaddamar da sabon samame, sun kama mutum 98 a Kano Jami’ar Tarayya ta Gashuwa za ta ba matar Tinubu digirin girmamawaAdadin waɗanda aka kashe mutum 32 da suka haɗa da maza da mata da ƙananan yara suna cikin wata mota ƙirar bas mai kujeru 18 daga unguwar Basawa da ke Ƙaramar hukumar Sabon Gari a Jihar Kaduna, domin halartar bikin aure a lokacin da suka haɗu da maharan.
Da yake gurfanar da waɗanda ake zargin a gaban babbar kotun jihar, lauya mai shigar da ƙara, S.I. Ikutanwa, ya nemi izinin kotun domin waɗanda ake zargin su ɗaukaka ƙara kan tuhume-tuhume huɗu da ake yi musu.
Sai dai lauyan da ke kare waɗanda ake zargin Garba Pwol, ya ƙi amincewa da buƙatar ƙarar, inda ya ce biyu daga cikin mutum 22 ƙananan yara ne, wanda hakan ya sa tuhume-tuhumen ba su da tushe.
A cewar lauyan da ke kare waɗanda ake zargin ’yan shekaru 13 ne da kuma 17, kuma doka ba ta yarda a gabatar ƙananan yara a irin wannan shari’ar ba. Lauyan da ke kare waɗanda ake ƙara ya buƙaci kotun da ta ba shi lokaci domin shigar da ƙara.
Da yake mayar da martani ga lauyan waɗanda ake tuhuma, lauyan mai shigar da ƙara ya ce, tun da biyu daga cikin waɗanda ake zargin ’yan ƙasa da shekaru 18 ne a cire sunayensu, sannan a bar sauran mutum 20 da ake tuhuma su amsa tuhumar.
Da yake tsokaci kan sharia’ar ga ɓangarorin biyu da suka gabatar, alƙalin kotun, Mai shari’a Boniface Ngyon, ya ce zai fi kyau kada a shigar da ƙarar nasu ranar Alhamis, maimakon haka za a yi gyara a ranar Juma’a, ban da ƙananan yara.