Kotun ƙoli ta tabbatar da Okpebholo a matsayin gwamnan Edo
Published: 10th, July 2025 GMT
Kotun Ƙoli ta tabbatar da Sanata Monday Okpebholo na jam’iyyar APC a matsayin sahihin Gwamnan Jihar Edo.
Wannan hukunci ya kawo ƙarshen shari’ar da ake yi biyo bayan zaɓen gwamnan jihar da aka yi a ranar 21 ga watan Satumba, 2024.
Jami’ar Tarayya ta Gashuwa za ta ba matar Tinubu digirin girmamawa Tinubu ne ya buɗe wa Buhari ƙofar zama shugaban ƙasa — HadimiKwamitin alƙalai biyar ƙarƙashin jagorancin Mai Shari’a Mohammed Garba ne, suka yanke hukuncin a ranar Alhamis.
Sun yi watsi da ƙarar da ɗan takarar PDP, Asue Ighodalo, ya shigar, kan cewar hujjojin da ya gabatar ba su da inganci.
Mai Shari’a Garba, ya ce Ighodalo da jam’iyyarsa PDP ba su kawo hujjoji masu ƙarfi da za su nuna cewa Okpebholo bai lashe zaɓen bisa ƙa’ida ba.
Ya kuma ƙara da cewa PDP ba ta bayyana yadda hukuncin kotun ƙasa da kotun ɗaukaka ƙara suka saɓa doka ba.
Tun da farko, PDP ta ce an samu matsaloli da kura-kurai a lokacin zaɓen, kuma ta nemi kotu ta soke sakamakon.
Amma kotun sauraron ƙorafe-ƙorafen zaɓe da kotun ɗaukaka ƙara sun yi watsi da ƙarar.
Hakan ne ya sa suka garzaya Kotun Ƙoli don neman haƙƙinsu.
Wannan hukunci na yau Alhamis, ya kawo ƙarshen duk wata shari’a da ta shafi zaɓen Gwamnan Jihar Edo, kuma Okpebholo zai ci gaba da zama gwamnan jihar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Monday Okpebholo Shari a Zaɓen Gwamna
এছাড়াও পড়ুন:
Abdullahi Ojlan Ya Sanar Da Kawo Karshen Fada Da Makami
Shugaban kungiyar Kurdawa ta kasar Turkiya ( PKK) Abdullah Ojlan ya sanar da kawo karshen amfani da makamai a fafutukar da kungiyarsu take yi na kare hakkokinsu a kasar Turkiya.
Shugaban kungiyar Kurdawan na Turkiya wanda yake tsare a kurkuku na shekaru masu tsawo, ya aiko da sako na bidiyo da a cikin ya ce; Har yanzu ina kan kiran da na yi a ranar 27 ga watan Febrairu na ajiye makamai”.
Ojlan ya kara da cewa; Muna sanar da kawo karshen amfani da makamai ne bisa radin kanmu, haka na kuma ya ce; Mun shiga Zangon aiki da doka da kuma siyasa da tsarin demokradiyya, wanda shi kanshi nasara ce mai dimbin tarihi ba asara ba.”
Kuniyar PKK ta kurdawan Turkiya dai ta yi fiye da shekaru 40 tana dauke da makamai a fadan da take yi da gwamnatin Turkiya. A watan Mayu da ya shude ne dai kungiyar ta sanar rusa kanta, sannan kuma ta sanar da Shirin ajiye makamanta na yaki.
Tun a 1999 ne gwamnatin kasar Turkiya take tsare da Abdullahi Ojlan.
An kafa kungiyar PKK ne a shekarar 1978, ya kuma fara kai hare-hare a cikin kasar Turkiya a 1984, da ya zuwa ajiye makaman kungiyar an kashe mutane fiye da 40,000.
A cikin shekarun bayan nan ne da aka bude tattaunawa a tsakanin kungiyar da kuma gwamnatin Turkiya akan batun kawo karshen tawaye, da samar da hanyoyin sulhi da zaman lafiya domin warware korafin Kurdawan.