Aminiya:
2025-08-01@09:20:06 GMT

NAJERIYA A YAU: Halin Da Matasa Suka Tsinci Kansu A Najeriya

Published: 27th, March 2025 GMT

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

A yau, da dama daga cikin matasan Najeriya na fama da matsaloli masu tarin yawa, musamman wajen ciyar da kansu da biyan buƙatunsu na yau da kullum.

Wannan na faruwa ne sakamakon halin da tattalin arziƙin ƙasa ke ciki, rashin aikin yi, da kuma tsadar rayuwa.

NAJERIYA A YAU: Yadda Ake Yi Wa ‘Yan Majalisar Ƙasa Kiranye NAJERIYA A YAU: Illar Sare Itatuwa Ga Sauyin Yanayi Da Lafiyarmu

Wasu daga cikin matasan sun kammala karatu, wasu kuma suna da sana’o’in hannu, amma duk da haka, rashin samun aikin da zai biya musu buƙatunsu yana ƙara jefa su cikin mawuyacin hali.

Wannan matsala na ci gaba da haddasa damuwa ga matasan ƙasar, inda da dama daga cikinsu ke fuskantar ƙuncin rayuwa sakamakon rashin tabbas a makomarsu.

Shirin Najeriya A Yau na wannan rana, zai nazarci irin waɗannan ƙalubale da matasa ke fuskanta, musamman a matakin farko na rayuwarsu.

Domin sauke shirin, latsa nan

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan Najeriya Najeriya a yau Rashin Aiki Tattalin Arziki

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu ya tsawaita wa’adin shugaban hukumar Kwastam

Shugaba Bola Tinubu ya ƙara wa Bashir Adeniyi, Shugaban Hukumar Kwastam ta Ƙasa, karin shekara ɗaya a kan wa’adin da ya kamata ya yi na shugabancin hukumar.

Mai magana da yawun shugaban ƙasa, Bayo Onanuga, ne ya bayyana haka cikin wata sanarwa a ranar Alhamis.

Mutum 9 sun rasu a hatsarin kwale-kwale a Jigawa NNPCL ya sake haƙa sabbin rijiyoyin man fetur 4 a Kolmani

A cewarsa, wa’adin Mista Adeniyi zai ƙare ne a ranar 31 ga watan Agusta, 2025.

Amma yanzu Shugaba Tinubu ya amince da ƙara masa shekara ɗaya, wanda hakan ke nufin zai ci gaba da zama a kan kujerarsa har zuwa watan Agustan 2026.

Sanarwar ta bayyana cewa ƙarin wa’adin zai ba shi damar kammala wasu muhimman ayyuka da yake yi.

Waɗannan ayyukan sun haɗa da gyara da inganta harkokin Kwastam, kammala wani shiri da zai sauƙaƙa kasuwanci a Najeriya, da kuma taimaka wa ƙasar wajen cika alƙawuran da ta ɗauka ƙarƙashin yarjejeniyar ciniki ta Afirka (AfCFTA).

Shugaba Tinubu, ya yaba da ƙwazon Mista Adeniyi da yadda yake gudanar da ayyukansa.

Ya ce ƙarin wannan wa’adin zai taimaka wajen inganta hanyoyin tara kuɗaɗen shiga a hukumar, da kuma tabbatar da tsaro a iyakokin Najeriya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Taɓarɓarewar Tarbiyyar Matasa A Arewa: Ƙalubalen Da Ke Gaban Iyaye Da Shugabanni
  • Mun ci ribar Naira biliyan 414 a cikin wata 6 a Najeriya – Kamfanin MTN
  • NAJERIYA A YAU: Me dokar kasa ta ce kan karin wa’adin aiki da Shugaban Kasa ke yi?
  • Tinubu ya tsawaita wa’adin aikin shugaban hukumar Kwastam
  • Tinubu ya tsawaita wa’adin shugaban hukumar Kwastam
  • NNPCL ya sake haƙa sabbin rijiyoyin man fetur 4 a Kolmani
  • Kamfanin NNPCL ya sake haka sabbin rijiyoyin man fetur 4 a Kolmani
  • Wasu ’yan siyasa na sukar Tinubu saboda ɗan Kudu ne — Onanuga
  • NAJERIYA A YAU: Tinubu ya yi wa Arewa adalci a ayyuka da mukamai — Bayo Onanuga
  • Shugaban SUBEB Yayi Alkawarin Bayar Da Tallafin Ilimi A Jihar Nasarawa