Aminiya:
2025-07-10@15:50:52 GMT

Jami’ar Tarayya ta Gashuwa za ta ba matar Tinubu digirin girmamawa

Published: 10th, July 2025 GMT

Jami’ar Gwamnatin Tarayya da ke Gashuwa (FUGA) a jihar Yobe za ta gwangwaje Uwargidan Shugaban Sasa, Sanata Remi Tinubu, da gwamnan Yobe, Mai Mala Buni, da wasu fitattun ’yan Najeriya shida da digirin girmamawa.

A cewar jami’ar, za a ba su shaidar ce saboda gudunmawar da suka bayar a bangarori da daman a ci gaban kasa.

Mataimakiyar Shugabar Jami’ar, Farfesa Maimuna Waziri ce ta bayyana hakan a lokacin da take ganawa da manema labarai a jami’ar.

Isra’ila ta kashe Falasdinawa 24 a Zirin Gaza Ba Tinubu kaɗai ne ya sa Buhari ya ci zaɓe a 2015 ba – Boss Mustapha

Ta ce za a karrama su ne a yayin bikin yaye dalibai karo na farko na jami’ar da zai gudana ranar Asabar mai zuwa.

Farfesa Maimuna ta ce za a karrama Sanata Remi ne da digirin digirgir ne na (D.Litt), yayin da Gwamna Buni da Ministan harkokin ’Yan Sanda kuma tsohon gwamnan Yobe, Sanata Ibrahim Geidam, dukkansu za su samu digirin digirgir ne a kan kwarewa kan harkokin mulki (DPA).

Ta kuma ce za a karrama tsohon Shugaban Majalisar Dattawa Sanata Ahmed Lawan da digirin digirgir bangaren kimiyya na D.Sc.

Haka kuma a cikin wadanda za a karrama akwai Mai shari’a Sidi Bage Muhammad da kuma Alhaji Bukar Goni Aji.

Farfesa Waziri ta ce jami’ar ta yaye dalibai kusan sau shida wadanda adadinsu ya kai 3,449 a tsangayoyin jami’ar guda hudu tun bayan da aka kafa ta.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gashuwa za a karrama

এছাড়াও পড়ুন:

Jami’an Leken Asirin “Shabak” Na Isra’ila Sun Kama Nasir Lahham Na Tashar Talabijin din Almayadin

Tashar talabijin din ‘almayadin’ ta bayar da labarin cewa; kungiyar leken asirin HKI ta cikin gida, “Shabak” ta kama shugaban ofishinta a Falasdinu dake karkashin mamaya  Nasir al-Lahham, a gidansa da yake a garin Beithlaham.

Majiyar ta kara da cewa; Jami’an kungiyar leken asirin ta “Shabakh” sun dade suna binciken dakin watsa labarin da Lahham yake watsa shirye-shiryensa.

Tashar ta “Almayadin’ dai ta bayyana cewa kamun da aka yi wa ma’aikacin nata yana a karkashin Takura mata ne da HKI take yi, domin a cikin watan Oktoba na 2023 ma dai jami’an tsaron sun kai hari cikin gidansa, su ka ci zarafin maidakinsa da kuma kama ‘ya’yansa Basil da Baasil.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Trump Ya Kakabawa Wata Jami’in MDD Takunkumi Bayan Ta Fallasa Laifukan HKI Da Hannun Amurka A Ciki
  • Jami’an tsaro sun hallaka ’yan bindiga 30 a Katsina
  • Tsohon Ɗan Takarar Gwamna A CPC, Haruna Sa’eed Kajuru, Ya Bukaci Gwamnatin Tarayya Ta Binciki Kisan ‘Yan Zariya  A Filato
  • Matar tsohon Gwamnan Adamawa ta sauya sheka daga PDP zuwa ADC
  • Za A Horas Da Jami’an Tsaron Sakkwato, Kaduna Da Benue Sabbin Dabarun Aiki
  • An ƙayyade maki da shekarun shiga jami’a a Nijeriya
  • An ceto mutum 6 daga hannun masu garkuwa a Kebbi
  • ASUU Ta Tsunduma Yajin Aiki A Faɗin Nijeriya
  • Jami’an Leken Asirin “Shabak” Na Isra’ila Sun Kama Nasir Lahham Na Tashar Talabijin din Almayadin