Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci ta Iran ya jaddada cewa; Mayar da martanin Iran ga ‘yan sahayoniyya sun murkushe girman kan makiya

Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci ta Iran Muhammad Baqir Qalibaf ya jaddada cewa: Martanin da Iran ta mayar wa yahudawan sahayoniyya a lokacin arangamar da suka yi a baya-bayan nan abin nuni ne, domin kuwa a duk tsawon tarihin haramtacciyar kasar Isra’ila ba ta taba samun irin wannan martanin mai gauni ba.

Ghalibaf, wanda ya karbi bakwancin jakadan Belarus a birnin Tehran, Dmitry Kaltsov, a jiya Laraba, ya yaba da matakin da gwamnatin Belarus ta dauka dangane da hare-haren da yahudawan sahayoniyya da Amurka suka dauika na kai wa cibiyoyin makamashin nukiliyar Iran hare-haren wuce gona da iri. Yana mai cewa, hare-haren da suka kai kan cibiyoyin makamashin nukiliyar kasar Iran na daga cikin munanan ayyukan da Amurka da yahudawan sahayoniyya suka aikata, idan aka yi la’akari da kasancewar Iran mamba a yarjejeniyar hana yaduwar makaman nukiliya ta NPT da kuma yadda ayyukan kasarta suke gudana  karkashin kulawar hukumar ta kula da makamashin nukiliya ta kasa da kasa ta IAEA.

Shugaban Majalisar Shawarar Musuluncin ya kuma jaddada cewa: A lokacin da aka kai wa Iran hari mahukuntan ta suna gudanar da shawarwari ne da Amurka kan batun shirin, har ma an sanya ranar da za a yi shawarwarin zagaye na shida. Ya kara da cewa: A cikin irin wannan yanayi, Iran ta ga irin yadda gwamnatin ‘yan sahayoniyya da Amurka suka kai wa Iran hari, yayin da a baya ta yi gargadin cewa, za ta mayar da martani mai karfi kan masu wuce gona da iri a duk wani harin da aka kai kan yankin kasarta. A kan haka, duniya ta shaida yadda Iran ta mayar da martani kan hare-haren wuce gona da irin gwamnatin ‘yan sahayoniyya da Amurka.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Shugaban Majalisar Shawarar

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Buni ya ware N5.8bn don biyan haƙƙin tsoffin ma’aikata a Yobe

Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni, ya amince da fitar da Naira biliyan 5.8 domin biyan haƙƙin tsoffin ma’aikatan gwamnati da suka yi ritaya a jihar.

Kwamishinan kuɗi na jihar, Mohammed Abatcha Geidam, ya ce wannan mataki na nuna yadda gwamnatin ke ƙoƙarin inganta rayuwar ma’aikatanta, musamman waɗanda suka bayar da gudunmawa wajen ci gaban jihar.

Farashin kayayyaki ya sauka zuwa kashi 18.02 a watan Satumba — NBS Dalilin da ya sa na bar tafiyar Kwankwasiyya – Farouk Lawan

Ya ce gwamnan ya bayar da umarni cewa daga yanzu, biyan haƙƙin tsoffin ma’aikata zai zama cikin jadawalin kuɗin wata-wata kamar yadda ake biyan fansho.

“Ina nufin daga yanzu za a riƙa biyan kudin a kowane wata tare da fansho, domin kauce wa taruwar bashi kamar yadda ya taɓa faruwa a baya,” in ji Kwamishinan.

Geidam, ya ƙara da cewa amincewar gwamnan babban mataki ne na tabbatar da cewa duk wani ma’aikaci da ya yi ritaya zai samu haƙƙinsa yadda ya dace.

“Hakan zai dawo da mutuncin tsoffin ma’aikata kuma ya tabbatar da cewa gwamnati tana nuna kulawa ga waɗanda suka yi mata hidima da gaskiya,” in ji shi.

Kwamishinan, ya bayyana cewa ma’aikatar kuɗi da ofishin shugaban ma’aikata suna aiki tare domin tabbatar da cewa an biya waɗanda abin ya shafa cikin lokaci ba tare da wata matsala ba.

Ya ƙara da cewa wannan mataki wani ɓangare ne na tsarin tattalin arziki da zamantakewa na Gwamna Buni domin tabbatar da jin daɗin al’ummar Jihar Yobe, musamman tsoffin ma’aikata da suka bayar da gudunmawa wajen ci gaban jihar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Isra’ila  Za Ta Sake Kai Hare-hare Idan Ta Karbi Dukkan Mutanenta Da Hamas Ta Kama.
  • Gwamna Buni ya ware N5.8bn don biyan haƙƙin tsoffin ma’aikata a Yobe
  • Ministan Yada Labarai Ya Bayyana Jihar Borno A Matsayin Mafi Juriya A Najeriya
  • Iran Ta Yi Allah Wadai Da Kalaman Kin Jinin Iran Da Trump Ya Yi A Majalisar Dokokin Isra’ila                             
  • Shugaban Kasar Columbia Ya Yi Dirar Mikiya Kan Donald Trump Kan Bai Wa Isra’ila Makamai
  • ’Yan Majalisar Tarayyar Kaduna 3 sun sauya sheka zuwa APC
  • Iran Ta Gabatar Da Shawarar Kulla Yarjejeniyar Tausayawa A Tsakanin Matan Duniya
  • Matakan Da Sin Ta Dauka Na Mai Da Martani Ga Bincike Mai Lamba “301” Da Amurka Ta Gudanar Sun Zama Wajibi Don Kare Hakkinta
  • Dan Majalisar Tarayyar Kaduna ya bar Jam’iyyar PDP
  • Yemen Ta Gargadi Isra’ila Kan Fuskantar Hare-Hare Idan Ta Karya Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta