Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci ya Bayyana Yadda Iran Da Mayar Da Martani Mai Gauni Kan Isra’ila
Published: 10th, July 2025 GMT
Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci ta Iran ya jaddada cewa; Mayar da martanin Iran ga ‘yan sahayoniyya sun murkushe girman kan makiya
Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci ta Iran Muhammad Baqir Qalibaf ya jaddada cewa: Martanin da Iran ta mayar wa yahudawan sahayoniyya a lokacin arangamar da suka yi a baya-bayan nan abin nuni ne, domin kuwa a duk tsawon tarihin haramtacciyar kasar Isra’ila ba ta taba samun irin wannan martanin mai gauni ba.
Ghalibaf, wanda ya karbi bakwancin jakadan Belarus a birnin Tehran, Dmitry Kaltsov, a jiya Laraba, ya yaba da matakin da gwamnatin Belarus ta dauka dangane da hare-haren da yahudawan sahayoniyya da Amurka suka dauika na kai wa cibiyoyin makamashin nukiliyar Iran hare-haren wuce gona da iri. Yana mai cewa, hare-haren da suka kai kan cibiyoyin makamashin nukiliyar kasar Iran na daga cikin munanan ayyukan da Amurka da yahudawan sahayoniyya suka aikata, idan aka yi la’akari da kasancewar Iran mamba a yarjejeniyar hana yaduwar makaman nukiliya ta NPT da kuma yadda ayyukan kasarta suke gudana karkashin kulawar hukumar ta kula da makamashin nukiliya ta kasa da kasa ta IAEA.
Shugaban Majalisar Shawarar Musuluncin ya kuma jaddada cewa: A lokacin da aka kai wa Iran hari mahukuntan ta suna gudanar da shawarwari ne da Amurka kan batun shirin, har ma an sanya ranar da za a yi shawarwarin zagaye na shida. Ya kara da cewa: A cikin irin wannan yanayi, Iran ta ga irin yadda gwamnatin ‘yan sahayoniyya da Amurka suka kai wa Iran hari, yayin da a baya ta yi gargadin cewa, za ta mayar da martani mai karfi kan masu wuce gona da iri a duk wani harin da aka kai kan yankin kasarta. A kan haka, duniya ta shaida yadda Iran ta mayar da martani kan hare-haren wuce gona da irin gwamnatin ‘yan sahayoniyya da Amurka.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: Shugaban Majalisar Shawarar
এছাড়াও পড়ুন:
Kazem Sajjadpour Ya ce: Iraniyawa Suna Daukan Tarayyar Turai Ma Goyon Bayan Harin Zaluncin Isra’ila Kansu
Mai ba da shawara ga ministan harkokin wajen kasar Iran ya bayyana cewa: Tarayyar Turai ta zama abokiyar gudanar da ta’addancin ‘yan sahayoniyya kan kasar Iran
Kazem Sajjadpour, mai baiwa ministan harkokin wajen kasar Iran shawara ya bayyana dabi’ar Turai a lokacin da yahudawan sahayoniyya suke kai wa Iran hari a matsayin abin da ba za a amince da shi ba, saboda matakin da suka dauka na goyon bayan ‘yan sahayoniyya lamarin da mayar da ita mai hannu wajen kai hare-haren.
Sajjadpour ya ce: Turai ba ta da wani matsayi a manufofin ketare na Amurka kuma Donald Trump bai ma ambaci Turai ba a cikin wannan tsari.
A wani taron karawa juna sani na yanar gizo da aka gudanar a ranar talata mai taken “Hanyar Haramtacciyar kasar Isra’ila kan Iran: Abubuwan da za a samu a nan gaba,” Sajjadpour, yayin da yake magana kan halaye da matsayin Turai a yakin kwanaki 12 da yahudawan sahayoniyya da Amurka suka kaddamar kan Iran, ya ce: “Turai na goyon bayan gwqwamnatin haramtaciyar kasar Isra’ila a kodayaushe, kuma shiru ko goyon bayan da wasu kasashen Turai suka yi kan zaluncin Isra’ila za su kasance da sun mummunar tasiri a cikin zukatan Iraniyawa.”