Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci ya Bayyana Yadda Iran Da Mayar Da Martani Mai Gauni Kan Isra’ila
Published: 10th, July 2025 GMT
Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci ta Iran ya jaddada cewa; Mayar da martanin Iran ga ‘yan sahayoniyya sun murkushe girman kan makiya
Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci ta Iran Muhammad Baqir Qalibaf ya jaddada cewa: Martanin da Iran ta mayar wa yahudawan sahayoniyya a lokacin arangamar da suka yi a baya-bayan nan abin nuni ne, domin kuwa a duk tsawon tarihin haramtacciyar kasar Isra’ila ba ta taba samun irin wannan martanin mai gauni ba.
Ghalibaf, wanda ya karbi bakwancin jakadan Belarus a birnin Tehran, Dmitry Kaltsov, a jiya Laraba, ya yaba da matakin da gwamnatin Belarus ta dauka dangane da hare-haren da yahudawan sahayoniyya da Amurka suka dauika na kai wa cibiyoyin makamashin nukiliyar Iran hare-haren wuce gona da iri. Yana mai cewa, hare-haren da suka kai kan cibiyoyin makamashin nukiliyar kasar Iran na daga cikin munanan ayyukan da Amurka da yahudawan sahayoniyya suka aikata, idan aka yi la’akari da kasancewar Iran mamba a yarjejeniyar hana yaduwar makaman nukiliya ta NPT da kuma yadda ayyukan kasarta suke gudana karkashin kulawar hukumar ta kula da makamashin nukiliya ta kasa da kasa ta IAEA.
Shugaban Majalisar Shawarar Musuluncin ya kuma jaddada cewa: A lokacin da aka kai wa Iran hari mahukuntan ta suna gudanar da shawarwari ne da Amurka kan batun shirin, har ma an sanya ranar da za a yi shawarwarin zagaye na shida. Ya kara da cewa: A cikin irin wannan yanayi, Iran ta ga irin yadda gwamnatin ‘yan sahayoniyya da Amurka suka kai wa Iran hari, yayin da a baya ta yi gargadin cewa, za ta mayar da martani mai karfi kan masu wuce gona da iri a duk wani harin da aka kai kan yankin kasarta. A kan haka, duniya ta shaida yadda Iran ta mayar da martani kan hare-haren wuce gona da irin gwamnatin ‘yan sahayoniyya da Amurka.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: Shugaban Majalisar Shawarar
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Mamayar Isra’ila Ta Amince Iran ta Kai Hare-Hare Kan cibiyoyin Sojojinta Guda Biyar
Gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ta yi furuci da cewa Iran ta kai hare-hare kan cibiyoyin sojojinta
Wani jami’in sojan gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ya yi furuci a ranar Talata cewa; Hare-haren da Iran ta kai a watan da ya gabata sun afkawa wuraren sojojin mamayar Isra’ila, matakin da tuni duniya ta amince da kai irin wadannan hare-hare kan cibiyoyin sojin mamaya.
Jami’in da ke magana da kamfanin dillancin labaran Reuters, ya ki bayar da karin bayani, ciki har da gano wuraren da abin ya shafa ko kuma irin barnar da harin ya yi ga kayayyakin aikin soja.
Iran ta kaddamar da hare-haren makamai masu linzami da jiragen sama marasa matuka ciki kan haramtacciyar kasar Isra’ila a watan da ya gabata a matsayin mayar da martani ga hare-haren ba-zata da gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ta kai a ranar 13 ga watan Yuni kan Iran wanda harin ya auna fitattun shugabannin sojoji da masana kimiyyar makamashin nukiliyar Iran.
Harin na Iran ya sha mai da hankali kan birnin Tel Aviv da Haifa, matsugunan yahudawan sahayoniyya ‘yan kaka gida musamman wuraren da suke dauke da mutane masu yawa da kuma yankin kudancin Falasdinu da aka mamaye kusa da Beersheba, inda ake da cibiyoyin soji.