HausaTv:
2025-05-24@22:51:16 GMT

Sudan : Janar al-Burhan Ya Shelanta ‘yantar Da Birnin Khartoum

Published: 27th, March 2025 GMT

Babban hafsan sojojin Sudan Janar Abdel Fattah al-Burhan, ya shelanta  ‘yantar da Khartoum Babban birnin kasar.

Wannan na zuwa ne bayan da tun da farko ya sanar da cewa dakarunsa sun kwato filin jirgin saman babban birnin, wuri mai matukar mahimmanci daga hannun dakarun ‘yan tawaye na RSF.

“An ‘yantar da Khartoum, an gama,” in ji shugaban na Sudan daga fadar shugaban kasa a wani jawabi da aka watsa a gidan talabijin na kasar.

Kazalika, wata sanarwa da sashen watsa labarai na majalisar rikon kwarya mai mulkin kasar ta fitar, ta ce Al-Burhan ya sauka a filin jirgin sama na kasa da kasa dake birnin Khartoum ta jirgi mai saukar ungulu a jiyan, jirgin da ya zamo na farko da ya sauka a filin, tun bayan barkewar tashin hankali a watan Afrilun shekarar 2023.

Daga nan ne kuma ya duba sassan rundunar sojin gwamnati dake tsaron filin jirgin kafin ya wuce zuwa fadar gwamnati.

Tun daga farkon shekarar 2024, dakarun sojin gwamnati na SAF ke ta kwace sassan kasar daban daban, musamman a birnin Omdurman na arewacin Khartoum, inda suka kwace kaso mai yawa na birnin, lamarin da ya karfafa ikonsu sama da na dakarun RSF a yankin.

A ranar Juma’a data gabata, sojojin na sudan sun ayyana kwace iko da fadar gwamnati, da wasu muhimman ofisoshin gwamnatin kasar dake Khartoum, wuraren da a baya suka kasance muhimman sassa da dakarun RSF ke rike da su a birnin na Khartoum.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Kotu ta bai wa EFCC izinin binciken sayar da filin musabaƙar Alƙur’ani na N3.5bn a Kano

Babbar Kotun Tarayya da ke Jihar Kano, ƙarƙashin jagorancin Mai Shari’a S.M. Shuaibu ta ƙi amincewa da buƙatar wasu mambobin Kwamitin Musabaƙar Alƙur’ani da ke son a hana EFCC bincike kan yadda aka sayar da wani fili mai darajar Naira biliyan 3.5.

Filin da ake magana a kai yana bayan titin Ahmadu Bello Way, kuma yana da faɗin hekta biyu.

Sojoji sun kashe mayaƙan ISWAP 16 a Borno An kama jami’in Hukumar NRC da laifin satar waya

Tsohon Gwamnan Sojan Kano, Kanal Abdullahi Wase ne, ya bayar da filin don a gina katafaren waje da za a riƙa gudanar da musabaƙar Alƙur’ani duk shekara.

Amma daga baya sai wasu mambobin kwamitin suka ga an gina gidaje 38 a filin ba tare da sanin su ba.

Hakan ne ya sa a ranar 11 ga watan Nuwamba, 2023, wasu daga cikin amintattun kwamitin suka kai wa EFCC ƙara, domin ta binciki yadda aka sayar da filin a ɓoye.

Waɗanda suka shigar da ƙarar sun haɗa da Sheikh Ibrahim Shehu Mai Hula, Sheikh Gwani Yahuza Danzarga, Tijjani Bala Kalarawi, Aliyu Harazimi, Barrister Saidu Koki, Ado Shehu Maibargo, Dokta Aliyu Darma, Tijjani Mai Lafiya Sanka, Alhaji Tukur Gadanya da Alhaji Sabiu Bako.

Sun buƙaci kotu ta hana EFCC gayyatarsu ko cafke su dangane da wannan batu, sun dogar da wasu sashe na kundin tsarin mulki da yarjejeniyar kare haƙƙin ɗan adam ta Afirka.

Amma kotu ta ce EFCC na da hurumin gudanar da bincike kamar yadda doka ta tanadar, kuma babu kotun da za ta hana hakan, musamman idan ana zargin aikata laifi.

Don haka, kotu ta bayyana cewa waɗana ake ƙara su biya Naira 250,000 ga waɗanda suka yi ƙararsu, saboda ɓata musu lokaci.

Lauyoyin da suka kare wanda ake ƙara – Sadiq Yahya da John Chukwu Eze – sun yaba da hukuncin kotun, yayin da lauyan masu ƙara, Yahaya Isa Abdulrasheed, ya ce za su ɗaukaka ƙara.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Halin da fasinjoji ke ciki bayan hatsarin jirgin sama a Ilori
  • Kamfanoni Masu Jarin Waje Sun Ci Gajiyar Tsarin Kasar Sin Na Samar Da Rangwamen Gwamnati Ta Musayar Sabbin Kayayyaki Da Tsofaffi
  • Kotu ta bai wa EFCC izinin binciken sayar da filin musabaƙar Alƙur’ani na N3.5bn a Kano
  • ‘Yan Sama Jannatin Shenzhou-20 Sun Kammala Aiki A Wajen Tashar Sararin Samaniyar Kasar Sin
  •  MDD Ta Nuna Damuwa Akan Tabarbarewar Yanayin “Yan Hijira A Gabashin  Kasar Chadi
  • Sojojin Yemen Sun Kai Wa Filin Jirgin Saman “Ben Gorion” Hari Sau Biyu A Yau Alhamis
  • An yi Jana’izar Shugaban Ƙungiyar Masu Shirya Finafinai ta Ƙasa a Zariya
  • Iran Ta Gamsu Da Lokaci Da Wurin Da Za A Gudanar Da Shawarwarinta Da Amurka Zagaye Na Biyar
  • Wani Mutum Ya Harbe Ma’aikatan Ofishin Jakadancin Isra’ila A Birnin Washington Na Amurka
  • Dakarun Yemen Sun Hana Zirga-Zirgan Jiragen Sama A Filin Jirgin Saman Ben Gurion Na Isra’ila