Aminu Ado ya soke hawan salla don gudun rikici a Kano
Published: 27th, March 2025 GMT
Sarkin Kano 15, Aminu Ado Bayero, ya soke shirinsa na gudanar da bikin hawan salla bayan shawarwari da dattawa da malaman addini suka ba shi.
Ya bayyana cewa matakin ya biyo bayan buƙatar tabbatar da zaman lafiya a jihar, biyo bayan shiga ruɗani da jama’a suka yi.
Hadimin Gwamnan Kano Tanka Galadanci ya rasu Majalisa ta amince da karatu na biyu kan ƙirƙirar sabbin Jihohi 4Wannan na zuwa ne yayin da aka shiga ruɗani a Kano saboda rikicin masarauta, biyo bayan mayar da Muhammadu Sanusi II a matsayin Sarkin Kano.
Tun farko, duka sarakunan biyu – Sanusi II da Aminu Ado Bayero, sun shirya gudanar da hawan salla, lamarin da ya haddasa fargaba a tsakanin al’umma.
A cikin wata sanarwa da ya fitar a daren Laraba, Sarki Aminu, ya ce ya ɗauki matakin ne bayan jin ra’ayin malamai da dattawa.
“Malamai da dattawa sun shawarce mu, kuma muna mutunta su. Don haka, bayan nazari tare da majalisar masarauta, mun yanke shawarar cewa mun janye domin zaman lafiya,” in ji shi.
Idan za a tuna, a makon da ya gabata ne, Aminu Ado, ya aike wa ’yan sanda takardar neman izinin gudanar da hawan salla, bayan da Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, ya umarci Muhammadu Sanusi II, ya shirya yin hawan salla a bana.
Sarkin ya jaddada cewa bikin hawan salla ba abu ne da ya zama wajibi ba idan zai iya haddasa rikici da asarar rayuka.
“Idan akwai fargabar cewa hawan salla zai haddasa tashin hankali da asarar rayuka ko dukiyoyi, to, yana da kyau a daina,” in ji shi.
A gefe guda, al’ummar Kano sun nuna damuwa kan yadda rikicin masarautar ke ci gaba da yin tasiri a rayuwarsu.
Ana sa ran wannan matakin zai rage fargabar da ake ciki, tare da tabbatar da zaman lafiya a Jihar Kano.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Aminu Ado Bayero Fargaba gwamna hawan salla Rikicin Masarauta Ruɗani Soke Hawan Salla hawan salla
এছাড়াও পড়ুন:
Espania Ta Soke Cinikin Makamai Na EUR Miliyon 700 Da HKI Saboda Kissan Kiyashi A Gaza
Gwamnatin kasar Spaine ta soke kontaragin sayan makama daga HKI wadanda yawansu ya kai Euro Miliyon 700, saboda kissan kiyashin da ke faruwa a gaza.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta bayyana cewa a jiya Litinin ne gwamnatin firay minister Pedro Sanchez ta bada wannan sanarwan ta kuma kara da cewa makaman su ne makamai masucilla rokoki samfurin Elbit kirar HKI.
Labarin ya kara da cewa Madrid ta soke wani kontaragi wanda ya kai Eur miliyon 287 da HKI. Na sayan garkuwan tankunan yaki wadanda za’a kerasu a kasar karkashin lacicin HKI a kasar Espania.
Banda haka firay minister Pedro Sanchez ya bukaci a haramta HKI daga dukkanin wasannin nakasa da kasa saboda kissan kiyashin da take aikata a gaza a ranar Lahadin da ta gabata.
Gwamnatin kasar ta Espania tabayyana cewa tanada shirin daukar wasu karin matakan kan HKI saboda kissan kiyashin datake aikatawa Gaza.
Daga cikinsu har da haramtawa dukkan yahudawan da suke da hannu cikin kissan kiyashin shiga kasar Espania .
Sannan akwai takunkuman tattalin arzikin na hana sayan dukkan kayakin da ake kerawa a kasar Falasdinu da aka mamaye.
Daga karshen gwamnatin kasar Espania ta zargi kasashen turai kan nuna fuska biyu a kissan kiyashin Gaza, idan an kwatanta da na Ukraine.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Makaman ‘Drons’ Na Yemen Sun Fada Kan Wurare Masu Muhimmanci A HKI September 16, 2025 Taron Doha: Daga matakin Allawadai zuwa matakan kalubalantar laifukan Isra’ila September 16, 2025 Ministan Tsaron Venezuela Ya Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Juyin Mulki A Kasar September 16, 2025 Pezeshkian: Ya kamata kasashen musulmi su yanke alaka da gwamnatin sahyoniya September 16, 2025 Bayanin Bayan Taron Doha Ya Yi Kira Da A Kafa Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kare Kai September 15, 2025 Fira Ministan Spain: Bai Kamata A Rika Barin “Isr’ila” Tana Shiga Gasar September 15, 2025 Shugaban Kasar Iran Ya Gana Da Sarkin Kasar Qatar A Birnin Doha September 15, 2025 Dan Kasar Iran Mai Kirkira Ya Sami Kyautar Yabo A Kasar China September 15, 2025 Fizishkiyan: Wajibi Ne Musulmi Su Hada Kai Domin Dakatar Da Laifukan HKI September 15, 2025 Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gana Da Takwarorinsa Na Qatar, Turkiyya, Pakistan Da Labanon A Doha September 15, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci