Kantoman Ribas ya dakatar da hadiman Fubara
Published: 27th, March 2025 GMT
Kantoman Jihar Ribas, Vice Admiral Ibok-Ete Ibas (mai ritaya), ya dakatar da dukkanin masu riƙe da muƙaman siyasa da jami’an gwamnatin jihar nan take.
A cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Laraba, Ibas, ya bayyana cewa ya ɗauki matakin ne bisa izinin da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya ba shi.
Gwamnatin Tarayya ta ayyana Litinin da Talata ranakun hutun sallah Ministan tsaro ya yi alƙawarin kawo sauyi a cibiyar horar da sojojiWaɗanda abin ya shafa sun haɗa da Sakatare na Gwamnatin jihar, Shugaban Ma’aikata, Kwamishinoni, shugabannin hukumomi, da masu ba da shawara na musamman.
Ya umarci duk waɗanda abin ya shafa da su miƙa ragamar ayyukansu ga sakatarorin ma’aikatunsu.
Ya ce hukumomin da babu sakatare, sai a bai wa babban darakta mafi girma ko shugaban gudanarwa.
Wannan umarni ya fara aiki daga ranar Laraba, 26 ga watan Maris, 2025.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: dakatarwa Muƙaman Siyasa umarni
এছাড়াও পড়ুন:
Trump ya dakatar da kamen baƙin haure a wasu wurare na Amurka
Shugaban Amurka Donald Trump ya umarci jami’an hukumar kula da shige-da-ficen-kasar da su dakatar da aikin samamen kama baƙin-haure ’yan ci-rani, a gonaki da otal-otal da ma gidajen sayar da abinci na fadin kasar.
Jaridar New York Times ta Amurka ta rawaito ma’aikatar tsaron cikin gida na tabbatar da samun umarnin, wanda aka mika shi ga hukumar kula da shige-da-fice da kuma ta yaki da fasa-kwauri, to sai dai kamfanin dillancin labarai na Reuters bai kai ga tabbatar da sahihancin umarnin ba.
’Yan bindiga sun kashe mutum 100 a Benuwe Wutar lantarki ta kashe mutum 5, ta jikkata 13 a GombeTun a lokacin yakin neman zaben shugabancin Amurka zango na biyu ,Mista Trump ya alkawarta korar bakin-hauren da suka shiga kasar ba bisa ka’ida ba.
To sai dai wannan mataki ya fuskanci kakkausan suka sakamakon yadda ake kame mutanen da ba su taba aikata laifin komai ba, musamman wadanda ke aiki a gonaki da sauran wurare, lamarin da ya janyo barkewar zanga-zanga a wasu sassan kasar.
Rahotanni sun tabbatar da cewa kawo yanzu an shafe kwanaki ana tarzoma a birnin Los Angeles na Jihar California ta Amurka, inda masu zanga-zanga ke dauki-ba-dadi da dakarun tsaron kasa da Shugaba Trump ya tura tun farko domin kwantar da zanga-zangar da ta barke sakamakon kamen bakin haure.