Kantoman Ribas ya dakatar da hadiman Fubara
Published: 27th, March 2025 GMT
Kantoman Jihar Ribas, Vice Admiral Ibok-Ete Ibas (mai ritaya), ya dakatar da dukkanin masu riƙe da muƙaman siyasa da jami’an gwamnatin jihar nan take.
A cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Laraba, Ibas, ya bayyana cewa ya ɗauki matakin ne bisa izinin da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya ba shi.
Gwamnatin Tarayya ta ayyana Litinin da Talata ranakun hutun sallah Ministan tsaro ya yi alƙawarin kawo sauyi a cibiyar horar da sojojiWaɗanda abin ya shafa sun haɗa da Sakatare na Gwamnatin jihar, Shugaban Ma’aikata, Kwamishinoni, shugabannin hukumomi, da masu ba da shawara na musamman.
Ya umarci duk waɗanda abin ya shafa da su miƙa ragamar ayyukansu ga sakatarorin ma’aikatunsu.
Ya ce hukumomin da babu sakatare, sai a bai wa babban darakta mafi girma ko shugaban gudanarwa.
Wannan umarni ya fara aiki daga ranar Laraba, 26 ga watan Maris, 2025.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: dakatarwa Muƙaman Siyasa umarni
এছাড়াও পড়ুন:
Ɗaukewar wutar lantarki ta tsayar da al’amura a Sifaniya da Portugal
Miliyoyin mutane sun auka cikin yanayi na duhu sakamakon ɗaukewar wutar lantarki a ƙasar Sifaniya da wasu sassan Portugal.
Lamarin ya shafi harkokin sufuri da sadarwa, da ma harkokin kasuwanci da dama.
Talata ce ɗaya ga watan Zhul Qi’ida — Sarkin Musulmi Yadda matar gwamna ta sa mata gasar haihuwar ’yan ukuSai dai asibitoci na gudanar da harkokinsu yadda aka saba saboda suna amfani da injinan janareto.
Shugabar gwamnati a yankin Madrid ta ce “abin da za mu yi shi ne mu nemi gwamnatin tarayya ta ayyana shiri na gaggawa don sojoji su kare doka da oda.”
Kamfanin lantarki na Sifaniya ya ce an gyara matsalar a yankunan arewaci da kudancin ƙasar.
Har yanzu dai ba a san abin da ya janyo matsalar ɗaukewar wutar ba, wadda ta shafi Portugal mai maƙwabtaka.
Bankin Sifaniya ya ce harkokin hada-hada ta intanet na ci gaba da aiki yadda ya kamata, sai dai an ambato wasu masu cirar kuɗi sun fuskanci ƙalubale a na’urar ATM.
A wani bidiyo da ya wallafa a shafin X, Mai Garin Madrid, Jose Luis Martinez-Almeida, ya buƙaci mazauna da su taƙaita zirga-zirgar saboda fargabar abin ka iya zuwa ya komo.
A Portugal kuwa, masu ruwa sun ce yana iya yankewa nan da kowane lokaci a yayin da jama’a ke tururuwar sayen ababen buƙata a manyan shaguna kamar tocilan, jannarera da batura.
Babban kamfanin lantarki na Portugal, EDP, ya shaida wa kwamstomi cewa babu takamaiman lokacin dawo da wutar da za a iya shafe sa’o’i kafin kammala gyara kamar yadda jaridar Publico ta ruwaito.