Gwamna Malam Umar Namadi na Jihar Jigawa ya jaddada kudirin gwamnatinsa na farfado da harkar kasuwanci mara shinge a Maigatari, wanda ya bayyana a matsayin muhimmin ginshikin bunkasar tattalin arziki, kasuwanci da masana’antu a jihar.

Ya bayyana hakan ne yayin wata ganawa da Kwamandan Yankin K da Jigawa na Hukumar Kwastam ta Najeriya, Kwamanda Dalhat Abubakar, wanda ya kai masa ziyarar ban girma a Fadar Gwamnati da ke Dutse.

Gwamna Namadi ya taya Kwamanda Abubakar murnar nadin nasa, tare da yaba wa hukumar Kwastam bisa goyon bayan manufofin cigaban jihar Jigawa, musamman wajen farfado da aikin Maigatari da aka yi watsi da shi.

Ya nuna godiya bisa goyon bayan  Kwamandan ya bayar, tare da yabawa da rahotannin da ke nuna yadda yake hada kai da tawagar tattalin arzikin jihar kan aikin.

Gwamnan ya bayyana tarihin  Maigatari Free Trade Zone, yana cewa ko da yake an kafa yankin fiye da shekaru 25 da suka wuce, an bar shi kara zube ba tare da cimma manufarsa ba.

Ya ce gwamnatinsa ta dauki matakai masu muhimmanci domin farfado da shi.

A cewarsa, an biya kudaden lasisi na doka, an yi shirin sake matsuguni ga mazauna yankin, kuma ana ci gaba da tattaunawa da masu zuba jari domin fara aiki da yankin.

Ya jaddada muhimmancin hadin gwiwa da hukumomin tarayya kamar Hukumar Kwastam don tabbatar da cewa yankin ya fara aiki gaba daya.

A nasa jawabin, Kwamanda Abubakar ya tabbatar da cewa Hukumar Kwastam ta shirya tsaf don fara aiki a Maigatari nan take, yana mai cewa sauran matsalolin da ke akwai na harkokin gudanarwa ne da na kayayyakin aiki, kuma za a iya magance su cikin sauki.

Ya yaba da jajircewar tawagar tattalin arzikin Jigawa, yana bayyana su a matsayin kwararru da kuma masu cikakken biyayya ga hangen nesan gwamna dangane da Maigatari.

Kwamanda Abubakar ya kuma jaddada irin fifikon da yankin Maigatari ke da shi, yana cewa kasancewarsa kusa da iyaka na ba shi gagarumar dama fiye da sauran yankuna, har da manyan cibiyoyin kasuwanci irin su Kano.

Ya bukaci ci gaba da hadin gwiwa tsakanin dukkan masu ruwa da tsaki don shawo kan sauran kalubale da kuma fitar da cikakken alfanu daga yankin.

A karshe, Gwamna Namadi ya tabbatar da cewa gwamnatinsa a shirye take ta dauki matakan da suka dace da shawarwari da tallafin da ake bukata don tabbatar da cewa Maigatari ya fara aiki gaba daya, tare da yin tasiri ga tattalin arziki.

 

Usman Muhammad Zaria 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa kwastam Maigatari tabbatar da cewa Hukumar Kwastam a Maigatari

এছাড়াও পড়ুন:

Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar

“Ana kiransa da suna dokar binciken tntanet ta tsoratarwa, wadda kasashen da suka ci gaba da dama suka dade da yin watsi da ita. A karni na 21, ba za a iya tunanin cewa gwamnatin Nijeriya za ta tauye ‘yancin fadin albarkacin baki, wanda shi ne ginshikin mulkin dimokuradiyya.”

Atiku ya ce duk wata doka da ke take ‘yancin ‘yan kasa na yin tsokaci mai muhimmanci game da shugabanninsu ko a hanyoyin sadarwar zamani ko ta hanyar magana ba dimokuradiyya ba ce kuma kai tsaye take hakkokin Dan’adam ne.

“A cikin shekaru biyu da rabi da suka gabata tun bayan da gwamnatin Tinubu ta fara daukan matakan da ke janyo kuncin tattalin arziki da yunwa da bakin ciki ga mutanen Nijeriya, mun shaida zanga-zanga da koke-koke daga ‘yan kasa da ba za su iya daukar mulkin rashin gaskiya ba. Duk da haka, maimakon sauraron ‘yan kasa sai gwamnatin ta zabi hanyar amfani da karfin hukumo da tsoratarwa wadda ta juya lamarin zuwa wani abu daban.

“Lallai abin bakin ciki ne na ganin ana take hakkin ‘yan kasa da kundin tsarin mulki ya tabbatar a lokacin da ya kamata dimokuradiyyarmu ta kasance mai bin tsari. Dole ne mu tunatar da gwamnatin Tinubu cewa babu gwamnati a lokacin da ta kasa kare ‘yancin ‘yan kasarta, komai karfinta kuwa. Yin haka abun ta da hankali ne kuma hakan yana nuna gazawar gwamnati a fili.”

Atiku ya ce tabbas gwamnati na da alhakin kula da doka da oda, babu ingantacciyar gwamnati da za ta harbi masu zanga-zangar lumana da harsashi mai rai ko ta boye a bayan dokoki tana musguna wa ‘yan kasa.

Ya ce rashin kulawar gwamnati Tinubu ga dokar kasa da kuma ci gaba da kin bin umarnin kotu sun zama shahararrun siffofinta mafiya suna a kasar nan a halin yanzu.

Tsohon mataimakin shugaban kasa ya kara da cewa tun farkon wannan gwamnati, kungiyar kare hakkin Dan’ada ta Amnesty ta soke wannan gwamnatin da take hakkin Dan’adam.

Ya ce haka ma wasu kungiyoyi masu muhimmanci kamar irinsu kungiyar ‘yan jaridu ta Nijeriya da kungiyar kare ajandar kafafen yada labarai sun yi korafi kan cin zarafin ‘yan jarida da ‘yan kasa ta hannun jami’an gwamnati.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato October 28, 2025 Manyan Labarai APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba October 27, 2025 Siyasa Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta October 24, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Namadi Ya Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • Gwamnatin Jigawa Ta Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • Iran ta damu da halin da ake ciki a yankin El Fasher na Sudan
  • Kwamitin Tsaron MDD ya goyi bayan shirin Morocco game da yankin Yammacin Sahara
  • Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC
  • Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar
  • Ya Kamata Shugaba Tinubu Ya Ƙulla Alaƙa Ta Kut-da-kut Tsakanin Hukumar Shige Da Fice Da Kwastam – Babandede
  • Masar da Eritrea Sun Tattauna Bukatar Tallafawa Kasar Sudan
  • Karamar Hukumar Gwarzo Ta Karfafa Yaƙi Da Miyagun Kwayoyi Da Shan Magani Ba Bisa Ka’ida Ba
  • Ci Gaba Da Killace Gaza Bayan Tsagaita Bude Wuta Ya Janyo Mutuwar Mutane 1000 A Yankin