Gwamna Malam Umar Namadi na Jihar Jigawa ya jaddada kudirin gwamnatinsa na farfado da harkar kasuwanci mara shinge a Maigatari, wanda ya bayyana a matsayin muhimmin ginshikin bunkasar tattalin arziki, kasuwanci da masana’antu a jihar.

Ya bayyana hakan ne yayin wata ganawa da Kwamandan Yankin K da Jigawa na Hukumar Kwastam ta Najeriya, Kwamanda Dalhat Abubakar, wanda ya kai masa ziyarar ban girma a Fadar Gwamnati da ke Dutse.

Gwamna Namadi ya taya Kwamanda Abubakar murnar nadin nasa, tare da yaba wa hukumar Kwastam bisa goyon bayan manufofin cigaban jihar Jigawa, musamman wajen farfado da aikin Maigatari da aka yi watsi da shi.

Ya nuna godiya bisa goyon bayan  Kwamandan ya bayar, tare da yabawa da rahotannin da ke nuna yadda yake hada kai da tawagar tattalin arzikin jihar kan aikin.

Gwamnan ya bayyana tarihin  Maigatari Free Trade Zone, yana cewa ko da yake an kafa yankin fiye da shekaru 25 da suka wuce, an bar shi kara zube ba tare da cimma manufarsa ba.

Ya ce gwamnatinsa ta dauki matakai masu muhimmanci domin farfado da shi.

A cewarsa, an biya kudaden lasisi na doka, an yi shirin sake matsuguni ga mazauna yankin, kuma ana ci gaba da tattaunawa da masu zuba jari domin fara aiki da yankin.

Ya jaddada muhimmancin hadin gwiwa da hukumomin tarayya kamar Hukumar Kwastam don tabbatar da cewa yankin ya fara aiki gaba daya.

A nasa jawabin, Kwamanda Abubakar ya tabbatar da cewa Hukumar Kwastam ta shirya tsaf don fara aiki a Maigatari nan take, yana mai cewa sauran matsalolin da ke akwai na harkokin gudanarwa ne da na kayayyakin aiki, kuma za a iya magance su cikin sauki.

Ya yaba da jajircewar tawagar tattalin arzikin Jigawa, yana bayyana su a matsayin kwararru da kuma masu cikakken biyayya ga hangen nesan gwamna dangane da Maigatari.

Kwamanda Abubakar ya kuma jaddada irin fifikon da yankin Maigatari ke da shi, yana cewa kasancewarsa kusa da iyaka na ba shi gagarumar dama fiye da sauran yankuna, har da manyan cibiyoyin kasuwanci irin su Kano.

Ya bukaci ci gaba da hadin gwiwa tsakanin dukkan masu ruwa da tsaki don shawo kan sauran kalubale da kuma fitar da cikakken alfanu daga yankin.

A karshe, Gwamna Namadi ya tabbatar da cewa gwamnatinsa a shirye take ta dauki matakan da suka dace da shawarwari da tallafin da ake bukata don tabbatar da cewa Maigatari ya fara aiki gaba daya, tare da yin tasiri ga tattalin arziki.

 

Usman Muhammad Zaria 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa kwastam Maigatari tabbatar da cewa Hukumar Kwastam a Maigatari

এছাড়াও পড়ুন:

Tsohon Ɗan Takarar Gwamna A CPC, Haruna Sa’eed Kajuru, Ya Bukaci Gwamnatin Tarayya Ta Binciki Kisan ‘Yan Zariya  A Filato

 

Tsohon ɗan takarar gwamna ƙarƙashin jam’iyyar CPC ta shuɗe a Jihar Kaduna, Alhaji Haruna Sa’eid Kajuru, ya bukaci Gwamnatin Tarayya ta gudanar da cikakken bincike kan kisan da aka yi wa wasu mazauna Zariya da suka je dauren aure a Jihar Filato kwanan nan.

 

Alhaji Kajuru ya yi wannan kira ne a lokacin da ya kai ziyara ta jaje ga iyalan waɗanda suka rasa ‘yan uwansu a Zaria, inda ya nuna alhini da ta’aziyya ga dangin waɗanda wannan al’amari ya shafa.

 

Tsohon Akanta Janar na Jihar Kaduna, Alhaji Haruna Kajuru, ya yi Allah-wadai da kisan, yana mai jaddada cewa babu wani mutum ko ƙungiya da ke da ikon da kundin tsarin mulki ya ba shi na kashe wani ɗan ƙasa.

 

Ya ce dole ne a kama masu hannu a kisan kuma a gurfanar da su a gaban shari’a domin hakan ya zama izina ga sauran mutane.

 

“Kundin tsarin mulki bai amince da kisan wani ɗan ƙasa ba. Dole ne mu tsaya tsayin daka wajen ganin an tabbatar da doka da oda a kasa,” in ji shi.

 

Alhaji Haruna Sa’eid Kajuru, wanda shi ne tsohon ɗan takarar gwamna na CPC a Jihar Kaduna, ya kuma yi kira ga gwamnatocin tarayya da na Jihar Kaduna su tallafa wa iyalan da abin ya shafa, domin rage musu raɗaɗin rashin ‘yan uwa da masu ciyar da su.

 

Kazalika, ya yi kira ga ‘yan Najeriya da su ci gaba da zauna lafiya da juna, yana mai cewa zaman lafiya da haɗin kai su ne ginshiƙan ci gaban tattalin arziki da zamantakewar al’umma.

 

Kisan da aka yi a Jihar Filato ya janyo tashin hankali da kiraye-kiraye daga sassa daban-daban na ƙasa kan buƙatar ƙara tsaro da tabbatar da adalci a cikin al’ummomin da abin ya shafa.

 

Rel: Adamu Yusuf

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwastam ta kama mazaƙutar jakai da aka yi yunƙurin safararsu
  • Ma’anar Sabon Tsarin Hadin Kan Mambobin Brics a Sabon Zamani Ga Dunkulewar Kasashe Masu Tasowa
  • Ma’aikatar Kasuwanci Ta Sin Ta Kara Kamfanoni 8 Na Yankin Taiwan Cikin Jerin Wadanda Aka Takaita Sayar Musu Kayayyaki
  • Tsohon Ɗan Takarar Gwamna A CPC, Haruna Sa’eed Kajuru, Ya Bukaci Gwamnatin Tarayya Ta Binciki Kisan ‘Yan Zariya  A Filato
  • HKI Ta Kashe Falasdianwa 6 A Gaza, Kuma Tsoffin Fursinoni
  • Firaminsitan Sin: Dole Ne Hadin Gwiwar Brics Ya Gaggauta Kafa Ka’idar Ciniki Da Tattalin Arzikin Duniya Mai Adalci Da Bude Kofa
  • HKI Tana Tana Son Ci Gaba Da Yaki Kuma Trump Yana Tare Da Shi
  • Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi
  • Gwamna Peter Mbah Ya Ƙaddamar Da Jiragen Kasuwanci 3 Na ‘Enugu Air’ Mallakin Jihar