Gwamna Namadi Ya Bukaci Hadin Gwiwar Hukumar Kwastam Don Farfado Da Yankin Kasuwanci Na Maigatari
Published: 10th, July 2025 GMT
Gwamna Malam Umar Namadi na Jihar Jigawa ya jaddada kudirin gwamnatinsa na farfado da harkar kasuwanci mara shinge a Maigatari, wanda ya bayyana a matsayin muhimmin ginshikin bunkasar tattalin arziki, kasuwanci da masana’antu a jihar.
Ya bayyana hakan ne yayin wata ganawa da Kwamandan Yankin K da Jigawa na Hukumar Kwastam ta Najeriya, Kwamanda Dalhat Abubakar, wanda ya kai masa ziyarar ban girma a Fadar Gwamnati da ke Dutse.
Gwamna Namadi ya taya Kwamanda Abubakar murnar nadin nasa, tare da yaba wa hukumar Kwastam bisa goyon bayan manufofin cigaban jihar Jigawa, musamman wajen farfado da aikin Maigatari da aka yi watsi da shi.
Ya nuna godiya bisa goyon bayan Kwamandan ya bayar, tare da yabawa da rahotannin da ke nuna yadda yake hada kai da tawagar tattalin arzikin jihar kan aikin.
Gwamnan ya bayyana tarihin Maigatari Free Trade Zone, yana cewa ko da yake an kafa yankin fiye da shekaru 25 da suka wuce, an bar shi kara zube ba tare da cimma manufarsa ba.
Ya ce gwamnatinsa ta dauki matakai masu muhimmanci domin farfado da shi.
A cewarsa, an biya kudaden lasisi na doka, an yi shirin sake matsuguni ga mazauna yankin, kuma ana ci gaba da tattaunawa da masu zuba jari domin fara aiki da yankin.
Ya jaddada muhimmancin hadin gwiwa da hukumomin tarayya kamar Hukumar Kwastam don tabbatar da cewa yankin ya fara aiki gaba daya.
A nasa jawabin, Kwamanda Abubakar ya tabbatar da cewa Hukumar Kwastam ta shirya tsaf don fara aiki a Maigatari nan take, yana mai cewa sauran matsalolin da ke akwai na harkokin gudanarwa ne da na kayayyakin aiki, kuma za a iya magance su cikin sauki.
Ya yaba da jajircewar tawagar tattalin arzikin Jigawa, yana bayyana su a matsayin kwararru da kuma masu cikakken biyayya ga hangen nesan gwamna dangane da Maigatari.
Kwamanda Abubakar ya kuma jaddada irin fifikon da yankin Maigatari ke da shi, yana cewa kasancewarsa kusa da iyaka na ba shi gagarumar dama fiye da sauran yankuna, har da manyan cibiyoyin kasuwanci irin su Kano.
Ya bukaci ci gaba da hadin gwiwa tsakanin dukkan masu ruwa da tsaki don shawo kan sauran kalubale da kuma fitar da cikakken alfanu daga yankin.
A karshe, Gwamna Namadi ya tabbatar da cewa gwamnatinsa a shirye take ta dauki matakan da suka dace da shawarwari da tallafin da ake bukata don tabbatar da cewa Maigatari ya fara aiki gaba daya, tare da yin tasiri ga tattalin arziki.
Usman Muhammad Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa kwastam Maigatari tabbatar da cewa Hukumar Kwastam a Maigatari
এছাড়াও পড়ুন:
Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo
Kakakin ma’aikatar tsaron kasar Sin Jiang Bin, ya ce a baya bayan nan babban jirgin ruwan dakon jiragen sama na kasar Sin mai suna Fujian, ya doshi yankin tekun kudancin kasar, inda ya ratsa ta zirin Taiwan, a kan hanyarsa ta gudanar da gwaje-gwaje da samar da horo.
Jami’in wanda ya bayyana hakan a Talatar nan, ya ce hakan bangare ne na ayyukan da aka saba gudanarwa lokaci-lokaci a wani bangare na kirar jirgin.
Jiang Bin, ya yi tsokacin ne yayin da yake amsa wata tambaya mai nasaba da hakan da aka yi masa, yana mai cewa, bulaguron jirgin ya dace da dokokin kasa da kasa da ayyuka masu nasaba, kuma ba shi da wata nasaba da tunkarar wani sashe. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp